Inter na son Inzaghi ya ci gaba da koci bayan kasa cin Champions League

Asalin hoton, Getty Images
Inter Milan na fatan Simone Inzaghi zai ci gaba da horar da ita, duk da kasa daukar Champions League, in ji shugaban kungiyar Giuseppe Marotta.
An caccaki kwazon kungiyar kan yadda Paris St Germain ta caskara Inter 5-0 a wasan karshe a babbar gasar tamaula ta Turai da suka yi a Munich.
Inzaghi wanda ya karbi aikin horar da Inter a 2021, ana ta alakanta shi da aiki a gasar tamaula ta Saudiyya a Al Hilal, sai dai shugaban ya ce yana sa ran zai gi gaba da zama da su.
Inzaghi ya dauki Serie A daya da Coppa Italia biyu a kaka hudun da ya yi a Inter.
Kungiyar Italiya ta doke Bayern Munich da Barcelona a hanyar da ta kai wasan karshe, kuma karo na biyu da ta kai karawar karshe a kaka uku, bayan da Manchester City ta yi nasara a kanta 1-0 a 2023 a Instanbul.
Rashin nasarar da Inter ta yi a hannun PSG na nufin ta kare kakar bana ba tare da daukar kofi ba, wadda ta yi ta biyu a kofin da Napoli ta lashe.
Haka kuma Inter ta yi rashin nasara a hannun AC Milan a zagayen daf da karshe a Coppa Italiya.