window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahotanni da bayanai dangane da mahimmman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Aisha Babangida, Khalifa Dokaji

  1. Majalisar dokokin Senegal ta amince da gurfanar da tsoffin ministocin ƙasar biyar a gaban kotu

    Majalisar dokokin Senegal ta kaɗa ƙuri'ar amincewa da gurfanar da tsoffin ministocin ƙasar biyar gaban wata kotu ta musamman don fuskantar tuhuma kan zargin cin hanci da rashawa.

    Ana zarginsu da yin almubazzaranci da kuɗaɗen da aka ware domin yaƙi da cutar ta Covid-19 daga shekarar 2020 zuwa 2021.

    'Yan adawar sun yi Allah wadai da tuhumar da ake yi wa ministocin.

    Ministocin biyar sun yi aiki a tsohuwar gwamnatin tsohon Shugaba Macky Sall - wanda shugaba mai ci Bassirou Diomaye Faye ya kayar.

  2. Zaɓen sabon fafaroma karramawa ce ga Amurka - Trump

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Trump ya bayyana zaɓar ɗan Amurka na farko a matsayin fafaroma da cewa karramawa ce ga Amurka.

    Ya ce yana farin cikin fatan ganawa da Fafaroma Leo, wanda a cewarsa, zai yi matuƙar amfani.

    Firaministar Italiya, Giorgia Meloni, ta bayyana kalaman sabon fafaroman a matsayin babban kiran zaman lafiya.

    Haka shi ma sarkin Sifaniya, ya ce kiran zaman lafiya da sabon fafaroman ya yi matuƙar ƙarfafa wa duniya gwiwa.

    Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce ƙasarsa na fatan samun goyon bayan fadar Vatican, a yunƙurin fadar na maido da zaman lafiya da adalci domin samun wanzuwar zaman lafiya.

  3. India ta zargi Pakistan da kai hari kan cibiyoyin sojinta

    India ta ce Pakistan ta kai harin roka a kan cibiyoyin sojin ta uku da suka yi iyaka da Kashmir.

    Idan aka tabbatar da faruwar harin, da alama zai ruruta rikicin da ke tsakanin ƙasashen biyu.

    An ga wasu mazauna Jammu, hedikwatar Kashmir, suna tururuwar ficewa daga yankin.

    Dama dai ministan tsaron Pakistan, Khawaja Muhammad Asif ya ce dakarun su za su mayar da martani ga India ta hanyar da ta dace.

    ''Ba za mu kai hari a kan fararen hula ba, ko kaɗan ba za mu yi haka ba, amma babu shakka za mu hari cibiyoyin sojin su'', kamar yadda ya yi ƙarin haske.

    Shi ma ministan harkokin wajen India, ya ce ƙasarsa za ta mayar da martani a kan duk wani hari daga Pakistan.

  4. Harin RSF ka kashe ƴanmata biyu a Khartoum

    fd

    Asalin hoton, AFP

    Wani hari da mayaƙan RSF suka kai a Sudan ya kashe wasu ƴanmata biyu a Khartoum babban birnin ƙasar.

    Ƙungiyar likitoci ta Duniya ta ce harin ya raunata wasu mutanen da dama, mafi yawan su kuma ƙananan yara ne.

    Rikicin Sudan ya ƙara ƙazancewa ne a ranar Lahadi, bayan da mayaƙan RSF suka ƙaddamar da hare-hare kan barikin soji da filin jirgin sama, lamarin da ya tilasta wa fararen hula yin ƙaura.

    Tuni dai ofishin jakadancin China a Sudan ya umarci ƴan Chinan su gaggauta ficewa har sai ƙura ta lafa.

  5. Bill Gates ya ce zai rabar da kusan duk dukiyarsa nan da shekara 20

    Bill Gates

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Bill Gates

    Ɗaya daga cikin manyan masu kuɗi na duniya, Bill Gates ya sanar da cewa zai sadaukar da kusan dukkanin dukiyarsa ga al'umma a cikin shekara 20 kafin ya rufe gidauniyarsa a shekarar 2045.

    Hamshaƙin mai arziƙin ya ware kimanin dala biliyan 200 domin tallafa wa ɓangaren lafiya da noma da kuma ilimi, inda ya ce ba ya son ya mutu a matsayin mai dukiya.

    Sai dai ya ce babu wata ƙungiya da za ta iya cike wagegen giɓin da aka samu sanadiyyar zabtare kuɗin tallafi da Amurka da Birtaniya da kuma Faransa suka yi.

    Gidauniyar ta kashe kuɗi dala biliyan 100 wajen bayar da tallafi a tsawon shekara 25 na ayyukan gidauniyar ta Gates Foundation.

  6. Sabon fafaroman cocin Katolika, Leo XIV ya gabatar da jawabinsa na farko

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Fafaroma Leo na 14 ya kammala jawabinsa na farko bayan zaɓen da aka yi masa a matrsayin wanda zai jagoranci mabiya ɗariƙar Katolika na duniya.

    ..

    Asalin hoton, Reuters

    A lokacin jawabin nasa ya jaddada muhimmanci hadin kai tsakanin al'umma.

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Bayan kammala jawabi, Leo ya gabatar da addu'a a taƙaice, yayin da dandazon mutane ke sowa.

  7. Leo XIV: Hoton farko na sabon fafaroma

    ...

    Asalin hoton, REU

    Wannan ne lokaci na farko da Robert Prevost ya fito bainar jama'a bayan zaɓen da aka yi masa a matsayin sabon fafaroma, wanda zai jagoranci mabiya ɗariƙar katolika na duniya.

    Lokacin da ya bayyana a kan baranda, abu na farko da Leo na 14 ya furta kafin fara jawabi shi ne "aminci ya tabbata a gare ku duka".

    Sabon fafaroman na da shekara 69 a duniya.

  8. Robert Prevost ne sabon fafaroma

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Fadar Vatican ta sanar da cewa Robert Prevost ne sabon fafaroma, wanda zai maye gurbin Fafaroma Francis.

    Shi ne fafaroma na farko daga ƙasar Amurka wanda zai jagoranci cocin na Katolika na duniya.

    Zai yi amfani da sunan Leo a muƙamin - wanda shi ne fafaroma na 14 da ya yi amfani da sunan.

  9. Hotunan yadda mutane ke murnar zaɓen sabon fafaroma

    Mutanen da suka yi dandazo a fadar Vatican sun ɓarke da murna yayin da suka tsinkayi farin hayaƙi ta saman ginin coci, wanda ke alamta kammala zaɓen sabon fafaroma, wanda zai jagoranci mabiya ɗariƙar Katolika na duniya.

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    ..

    Asalin hoton, Reuters

    Mutane sun riƙa kaɗa tuta sun rungumar juna yayin da ake jiran bayyana sunan wanda zai muƙamin.

    ...

    Asalin hoton, Reuters

  10. Me ya rage bayan zaɓen sabon Fafaroma?

    Yanzu haka dai masu zaɓen sabon fafaroma sun kammala aikinsu na zaɓen wanda zai gaji Fafaroma Francis, yanzu kuma za su fara aikin bayyana wa duniya ko wane ne shi.

    Bayan fitar farin hayaƙi, wanda ke alamta zaɓen sabon fafaroma, nana da awa ɗaya ake sa ran sabon fafaroman zai bayyana a kan barandar ginin fadar da ke kallon dandalin St Peter.

    Amma a halin yanzu za a shigar da sabon fafaroman wani ɗaki da ke kusa da inda aka yi zaɓen, inda a nan ne zai sanya fararen kaya na muƙamin fafaroma.

    Jagoran malaman da suka yi zaɓen ne zai fito tare da faɗin "Habemus Papam" - wato "mun samu sabon fafaroma" a harshen Latin.

  11. An zaɓi sabon Fafaroma

    ...

    Asalin hoton, EBU

    Yayin da farin hayaƙi ya ɓullo ta bututun hayaƙi na saman rufin cocin Sistine da ke fadar Katolika, hakan na nuna cewa an kammala zaɓen sabon Fafaroma wanda zai jagoranci cocin katolika na duniya.

    Sabon Fafaroman shi ne zai maye gurbin marigayi Fafaroma Francis, wanda ya rasu.

    Ya zuwa yanzu ba a sanar da wanda aka zaɓa a matsayin sabon fafaroman ba, amma ana sa ran sanin hakan nan ba da jimawa ba.

  12. Babu tabbas game da halin da fursunonin Gaza uku ke ciki - Netanyahu

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa akwai rashin tabbas game da halin da wasu uku daga cikin fursunoni Gaza 24 da aka yi imani suna raye a hannun Hamas ke ciki a Gaza.

    Benjamin Netanyahu ya ce yana da tabbacin cewa fursunoni 21 suna raye, amma ba a san halin da wasu uku ke ciki ba.

    Ya bayyana hakan ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya ce fursunoni 24 suna raye mako guda da ya wuce, amma yanzu adadin ya koma 21.

    Ya faɗi hakan ne yayin wani taro a Fadar White House ranar Talata, ba tare da wani ƙarin bayani ba.

    An kuma buƙaci Netanyahu a taron da ya dakatar da shirinsa na ƙara faɗaɗa hare-haren Isra’ila a Gaza, tare da ƙulla yarjejeniya da Hamas don dawo da sauran fursunoni 59 da ke raye da kuma waɗanda suka mutu.

  13. Me Jonathan ya ce kan zargin mayar da Najeriya tsarin jam'iyya guda?

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Bayan tsawon lokaci ba a ji ta bakinsa ba dangane da faruwar al'amuran siyasa, tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Ebele Jonathan ya ɓara inda ya yi gargaɗin cewa "abu ne mai haɗari ɗora Najeriya a kan turbar jam'iyya guda ɗaya".

    Ba kasafai dai ake jin bakin Goodluck Jonathan ba a al'amura kasancewarsa mutum mai kawaici da rashin son yawan magana.

    To sai dai a ranar Larabar nan, tsohon shugaban na Najeriya yayin wata lacca da aka shirya a Abuja domin tuna wa da marigayi Edwin Clerk, dattijo ɗan ƙabilar Ijaw wanda ya rasu yana da shekara 97, Jonathan ya ja hankalin gwamnati da jam'iyya mai mulki ta APC da ake zargi da mayar da ƙasar ƙarƙashin tsarin jam'iyya guda.

    Ci gaban labarin - /hausa/articles/c2kqjx494d3o

  14. Wane ne zai iya zama sabon Fafaroma?

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana muhawara kan ƴan takara da dama wadanda ake tunanin za su iya gadar Fafaroma Francis domin jagorantar Chocin Katolika. Ga bayanan manyan ƴan takara da aka fi tunanin ka iya yin nasarar zama Fafaroma:

    • Cardinal Pietro Parolin: Ya kasance sakataren kula da harkokin waje a Vatican ƙarƙashin fafaroma Francis wanda ya naɗa shi a matsayin mai bashi shawara.
    • Peter Kodwo Appiah Turkson, ya kasance dan Ghana na farko da aka nada babban limami a lokacin Fafaroma John Paul a 2003, sannan an yi ta hasashen zai iya zama fafaroma saboda karɓuwarsa a wajen masu buga littafi a 2013, inda kuma aka zaɓi Fararoma Francis a maimakon shi.
    • Cardinal Fridolin Ambongo Besungu: Shi ma daya daga cikin manyan ƴan takarar, ya kuma fito ne daga jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo inda ya kasance Arc Bishop a Kinsasha tsawon shekara bakwai.
    • Cardinal Luis Antonio Gokim Tagle: ana yi masa kallon wanda ka iya zama zaɓin masu zaɓen, kasancewar Cocin Katolika, na da tasiri a ƙasarsa ta Phillippines, inda kashi 80% na al'ummar ƙasar ke bin ɗariƙar ta katolika.
    • Cardinal Robert Prevost daJoseph Tobin, an sha ambata su a jerin wadanda za su iya zama Fafaroma a duk lokacin da aka zo irin wannan lokaci, wanda daya daga cikin su zai iya zama dan Amurka na farko da zai zama Fafaroma.
    • Mene ne ya yi ajalin fafaroma Francis kuma wace wasiyya ya bari?
    • Me ya sa Fafaroma Francis ya zaɓi a binne shi a wajen fadar Vatican?
  15. An hangi fitar baƙin hayaƙi a fadar Vatican bayan kaɗa ƙuri'a ta uku

    .

    Asalin hoton, bbc

    Bayanan hoto, .

    An ji sowar "hayaƙi, hayaƙi" a dandanlin St Peters, yayin da aka ga fitar sabon labari na farko na abin da ke faruwa a cikin majami'ar Sistine, bayan fitar hayaƙi daga wajen fitar da hayaƙi, mintuna da suka gabata.

    Mutane sun yi ta tururuwar zuwa ɗaukar hoto, da wayoyinsu, tare da mastawa don su ga abun da ke faruwa.

    An dai shafe kwanaki biyu a lokaci na ƙarshe da aka zaɓi Francis a 2013, bayan kaɗa ƙuri'u biyar.

    A 2015 lokacin da aka zaɓi Fafaroma Benedict XVI, shi ma kwanaki biyu aka yi, kuma ƙuri'u huɗu aka kaɗa, yayin da na Fafaroma John Paul da aka yi a 1978, kwanaki uku kawai aka ɗauka, sannan aka kaɗ ƙuri'u 8.

  16. "Idan Pakistan ta takale mu za mu mayar da martani"

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, .

    Ministan harkokin wajen Indiya S Jaishankar ya ce Indiya bata da "niyar ta'azarar al'amura" tsakanin su da Pakistan, idan kuma har ta kai musu hari, babu makawa "za su mayar da zazaafan martani".

    Jaishankar ya bayana hakan ne a yayin wani taro haɗin guiwa na Iran da Indiya da ya gudana a Delhi, inda ministan harkokin wajen ƙasar Iran Abbas Araghchi ya kai ziyara ƙasar. Ƙasashen biyu na bikin ciki shekaru 75 da ƙawance.

    A cewar Jaishankar "ka kawo mana ziyara Indiya a lokacin da muke mayar da martani kan wani hari na rashin imani da yan ta'adda. Ya na yi masa bayani ne, kan harin da aka kai a ƙarshen watan da ya gabata, kan masu yawon buɗe idanu a Pahalgam. Indiya dai ta zargi mayaƙan sa kai, da ke samun goyan bayan Pakisatan da kai shi, sai dai Islamabad ta musanta zargin.

    "Ba niyyar mu ba kenan na ta'azara al'amura ba. Amma idan aka kai mana hari, babu ko kokonto, za mu mayar da kakausan martani."

    Jainshankar ya sanar da takwaransa na Iran cewar, a matsayin ku na maƙotan mu, da abokan hulɗar mu, da kuka fahimci kan lamarin.

    A baya dai Iran ta yi yunƙurin shiga tsakani a rikicin da Indiyan ke yi da Pakistan.

  17. An samu rashin fahimta tsakanin ƴan majalisa da ministan tsaron Najeriya kan tsaro

    .

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, .

    Ministan tsaron Najeriya, Mohamamd Badaru Abubakar ya ce sauya dabarun tsaro ne abun da ya kamata a mayar da hankali ba wai taro kan tsaro da majalisar dattawan ƙasar ta nemi a yi ba.

    Haka kuma ya musanta zargin da majalisar wakilan ƙasar ta yi na cewar ƴan bindiga na amfani da makaman da suka fi na jami'an tsaron ƙasar.

    A ranar Talata ne dai majalisar dattawan Najeriya ta buƙaci da a shirya wani taro kan harkokin tsaro, don samar da hanyoyin magance matsalar.

    Sai dai a yayin ganawa da manema labarai na ministoci da ya gudana a jiya Laraba ministan tsaron na Najeriya Mohammad Badaru Abubakar ya ce sake dabarun yaƙi da matsalar tsaro ya kamata a yi ba wai taro ba a halin da ake ciki a ƙasar.

    "Idan ka yi taron ƙasa kan tsaro, mutane za su zo, su fadi abin da suke so, mu kuma za mu ɗauka, sannan sai mu koma, don sake sabunta tsarin mu na tsaro, sannan sai babban hafsan tsaron ƙasa shi ma ya bayar da umarni bisa dabaru da tsarin da aka bayar. Abun da majalisar suke ƙoƙarin yi, shi ne, su tara mutane su tattauna kan batutuwa. Za ka ji maganganu iri-iri." in ji Badaru.

  18. Hare-hare a Pakisatan da Indiya sun tilasta wa al'ummar Kashmir barin gidajensu

    .

    Asalin hoton, Aamir Peerzada/BBC

    Bayanan hoto, .

    Gwamman mazauna birnin Poonach da ke yankin ƙashmir da ke ƙarƙashin ikon Inidiya ne dai suka fara barin muhallansu don kaucewa rikicin da ya fara ƙamari a iyakokin Pakistan da Indiya.

    Indiya ta ce tsawon makonni biyu kenan, da kai wani hari kan masu yawon buɗe idanu a Pahalgam, Pakistan na ci gaba da karya yarjejeniyar zaman lafiya da ɓangarorin biyu suka cimma, inda suke ta kai hare-hare kan iyakar ta Indiya. Wani zargi da Pakistan ɗin ta musanta

    Wasu mazauna yankin sun shaidawa BBC cewar, kai hare-haren ya yi ƙamari ne bayan da Indiya ta kai wani hari a safiyar ranar Laraba, kan Pakistan.

    "Ni dai na ji wata irin muguwar ƙara, inda na fita a guje rike da jariri na da bai fi wata ɗaya da haihuwa ba a hannu. Na ji tsoro,' in ji Sobia.

    ita ma Sufreen Akhtar, ta ce ita da iyayen ta da ƴan uwan ta sun bar gida bayan da aka sake harbo wani bom ya faɗa kan gidansu.

    "Ba mu iya samun mota ba, haka muka taka a ƙafa tsawon sama da milimita ɗaya, har muka kawo inda muke. Na yi kuka sanda muke hanya, don an yi ta harba bom," in ji ta.

    Hukumomi a yankin sunce kimanin mutu 80 ne suka bar gidajensu, sannan akwai yiwuwar samun wasu.

  19. Tinubu ya umarci a cire shingayen da ke kan iyakokin Najeriya

    .

    Asalin hoton, Nigeria State House

    Bayanan hoto, .

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya kafa wani kwamitin shugaban ƙasa na musamman da zai cire dukkan wasu shingaye da ake da su a kan iyakokin ƙasar don sauƙaƙa harkokin cinikayya da tafiye-tafiye.

    Amabasada Musa Nuhu wakilain Najeriya a ƙungiyar Ecowas ne ya sanar da hakan, a wata ziyara da ya kai iyakar Najeriya da Jamhuriyar Binin wato Same a ranar Laraba.

    Masu ababen hawa sun sha kokawa da yadda ake karɓar kudade a hannunsu, a dukkan wani shinge da suka zo wucewa akan hanayr ta Iyakar ta Seme wato iyakar Najeriya da jamhuriyar Benin.

    Ambasada Nuhu ya ce "hanyar ta kasance wadda aka fi zirga-zirga a Afrika, musamman wajen fitarwa da shigar da kaya, da shige da ficen al'umma. Zamu iya ganewa idan ana tafiye tafiye ba tare da shinge ba a yankin Afrika ta Yamma", in ji shi.

    "Mun ji dukkan ƙorafe-ƙorafen da ake yi kan hanyar na yadda shingayen da jami'an tsaro da na jami'an hana fasa ƙauri ke sanyawa ke shafar matafiya da kayan da masu shigowa ko fitar da kaya.

    Shugaban hukumar Ecowas Omar Alieu Touray ya yi, Allah wadai kan yadda jamai'an tsaron da ke kula da shingayen da ke hanyar ke ƙarɓar kuɗi a hanun al'ummar ƙasashe daban-daban da ke shige da fice a ƙasar, wanda ya ce hakan, ya saɓa da shirin ECOWAS na haɗe yankin wuri ɗaya

  20. Assalamu alaikum

    Ma'abota BBC Hausa barkanmu da hantsin yau Alhamis.

    Sannunmu da sake haɗuwa a shafin labarai kai-tsaye, wanda zai kawo rahotonnin abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, musamman a Najeriya da Nijar da maƙwabtansu.

    Ku kasance da mu