Rufewa
Jama'a a nan muka kawo ƙarshen wannan shafin na labaran kai-tsaye. Sai kuma gobe Laraba idan Allah ya kai mu.
A madadin sauran abokan aiki, ni Isiyaku Muhammed nake cewa mu kwana lafiya.
window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);
Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 20/05/2025
Haruna Ibarhim Kakangi da Aisha Babangida
Jama'a a nan muka kawo ƙarshen wannan shafin na labaran kai-tsaye. Sai kuma gobe Laraba idan Allah ya kai mu.
A madadin sauran abokan aiki, ni Isiyaku Muhammed nake cewa mu kwana lafiya.
Asalin hoton, Getty Images
Har zuwa yanzu ba a fara raba kayan agaji Zirin Gaza ba, kamar yadda kakakin Majalisar Ɗinkin Duniya, Stephane Dujarric ya bayyana.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake murnar fara shigar da kayan agaji yankin na Falasɗinu ta ɓangaren Kerem Shalon, wanda yanki da ke tsakanin kudancin Gaza da Isra'ila.
"A yau daga cikin wakilanmu sun jira na sa'o'i sosai domin samun lasisin shigar da kayan agaji ta yankin Kerem Shalon domin karɓo abinci masu gina jiki. Amma abin takaicin shi ne ba su kawo mana kayan abincin ba," in ji Dujarric a ganawar Majalisar Ɗinkin Duniya da manema labarai.
Ya ƙara da cewa, "an shiga da kayan agaji Gaza," amma ya ƙara da cewa wakilan Majalisar Ɗinkin Duniya sun jira, "amma ba su samu karɓar kayan ba a gidajen ajiyarsu da ma cibiyoyin rabo."
Tun da farko, Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce Isra'ila ta amince a shigar da motoci 100 na kayan abinci zuwa Gaza bayan hanawa na mako 11.
Asalin hoton, Reuters
Sanarwar Joe Biden cewa yana ɗauke da cutar ƙasan mafitsara ta jawo tambayoyi kan irin yanayin rashin lafiyar da ya sha a zamanin da yake shugabantar Amurka.
A wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, ofishin Biden ya ce tsohon shugaban mai shekara 82 yana fama da cutar kansar, wadda ta bazu zuwa ƙasusuwarsa, kuma ba a gano ba a cikin lokaci.
Wasu likitoci sun bayyana mamakinsu kan yadda cutar ta bazu zuwa ƙasusuwa, amma kuma ba iya a ganowa da wuri ba.
Wasu kuma suka ce dama kansa tana ya iya bazuwa cikin sauri ba tare da nuna alama ba - sannan wasu suka ce maza da suka haura shekara 70 ba su cika zuwa gwaji ba.
Shugaba Donald Trump ya ce ya kamata a ce wanda ya gada ya bayyana wa jama'a gaskiyar halin da yake ciki - inda yake nufin cewa an yi rufa-rufa ne game da cutar, duk da bai bayar da dalili ba.
Asalin hoton, AFP
Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta musanta cewa ta taka rawa a harin da aka kai a farkon wannan watan a garin Port Sudan wanda ta kasance hedikwatar gwamnatin Sudan tun bayan da yaƙi ya ɓarke a ƙasar sama da shekara biyu da suka gabata.
A ranar Litinin jakadan Sudan a Majalisar Ɗinkin Duniya ya yi ikirarin cewa jiragen yaƙi ne da suka tashi daga sansanonin masarautar suka kai harin.
Daga nan ne Sudan ta yanke hulɗar diflomasiyya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, tana mai cewa masarautar na taimakawa abokan hamayyar sojojin ƙasar, wato dakarun Rapid Forces, da makamai na zamani.
Asalin hoton, Getty Images
Gwamnatin Najeriya ta sanar da shirinta na sayar da gidaje guda 753 da ta ƙwato daga tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele, waɗanda suke cikin kadarorin da Hukumar EFCC ta ƙwato daga hannun masu almundahana da kuɗin ƙasar.
Ministan gidaje na Najeriya ne ya tabbatar da hakan a ranar Talata a lokacin da yake karɓar takardun gidajen daga hannun EFCC, kamar yadda tashar talabijin ta Channels ta ruwaito.
A wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama'a na ma'aikatar, Salisu Haiba ya fitar, ya ce, "ma'aikatar gidaje ta karɓa gidaje 753 da suke Abuja waɗanda Hukumar EFCC ta ƙwato daga tsohon babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele."
Ministan ma'aikatar, Ahmed Dangiwa, ya yaba wa ƙoƙarin Hukumar EFCC ɗin wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.
Asalin hoton, Godswill Akpabio
Shugaban majalisar dattawa ta Najeriya, Sanata Godswill Akpabio ya ce ba a zaɓe su - ƴan majalisa - ba domin su je su riƙa rigima da ɓangaren zartaswa, inda ya ce aikinsu shi ne yin dokokin da za su ciyar da ƙasar gaba.
Akpabio ya bayyana haka ne a tsakuren bidiyon shiri na musamman da aka domin bikin cika shekara biyu na gwmanatin Bola Tinubu.
Da yake magana game da amfanin haɗin kai tsakanin ɓangarorin biyu, ya ce, "idan ka lashe zaɓen majalisa, ko dai ta dattawa ko ta wakilai, waɗanda kake wakilta ba za su ba ka safar hannun dambe ba. Ba dambe muka zo yi ba, mun zo ne domin gudanar da ayyukan da za su ciyar da Najeriya gaba."
Shugaban majalisar ta nanata cewa akwai alaƙa mai kyau da fahimta tsakanin majalisa da ɓangaren zartaswa a shekara biyu da suke gabata.
"Idan ka ƙarar da lokacinka wajen rikici da ɓangaren zartaswa, waye zai yi wa Najeriya aikin":[]}