Boko Haram na sake taruwa a yankin tafkin Chadi da tsaunukan Mandara - Zulum

Asalin hoton, Zulum
Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya bayyana damuwarsa kan yadda ya cce mayaƙan Boko Haram na sake taruwa a yankin Tumbus da ke yankin tafkin Chadi da tsaunukan Mandara a dajin Sambisa.
Zulum ya bayyana hakan ne a birnin Maiduguri lokacin da yake karɓar baƙuncin ministan tsaron Najeriya, Badaru Abubakar da babban hafsan tsaron ƙasar, Janar Christopher Musa, da sauran manyan sojojin ƙasar, kamar yadda Jardiar Daily Trust ta ruwaito.
Haka kuma gwamnan ya yaba da ƙoƙarin jami'an tsaron ƙasar a yaƙin da suke yi da mayaƙan na Boko Haram a yankin arewa maso gabashin Najeriya.
Gwamnan Zulum ya ce Mayaƙan Boko Haram na yawonsu a yankin tafkin Chadi ba tare da wata tsangwama ba, don haka ya ce akwai buƙatar sojojin su ƙara ƙaimi wajen kakkaɓe su.