window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 28/05/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Usman Minjibir da Aisha Babangida

  1. PDP za ta ɗauki mataki kan rufe babban ofishinta

    PDP

    Asalin hoton, PDP

    Babbar jam'iyyar hammaya ta PDP a Najeriya ta ce tana nazari kan matakin da ya kamata ta ɗauka game da rufe hedikwatarta da hukumar kula da birnin Abuja ta yi.

    Hukumar kula da birnin Abuja dai ta rufe gine-gine sama da dubu huɗu waɗanda ta ce sun karya dokar biyan harajin ƙasa.

    PDP ta ce za ta bi diddigi domin gane abin da ya janyo tsaiko wajen buɗe ofishin nata duk kuwa da umarnin da shugaba Tinubu ya bayar na a buɗe wuraren da aka rufe saboda rashin biyan harajin ƙasa a birnin Abujan domin ba su damar biya.

    Yusuf Dingyadi babban mataimaki ne ga shugaban jam'iyyar PDP kan sadarwa, kuma ya shaidawa BBC cewa idan har shugaban ƙasa ya bayar da umarnin buɗe wuraren da aka rufe to ya kamata su gani a ƙasa.

    Ya ce ''Mu mun san mun bi duk ƙa'idojin da suka dace.''

    ''Shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa ya bayar da umarni ga sashin shari'a na jam'iyyar da kuma sashi kuɗi domin su yi nazari kan abin da ya kamata a yi, kuma da sun ƙare za mu fitar da sanarwa.''

    Ya kuma bayyana cewa su a wajen su, rashin buɗe ofishin nasu ƙin biyayya ne ga umarnin da shugaban ƙasa ya bai wa ministan birnin na Abuja.

  2. Namibia ta yi bikin tunawa da kisan kiyashi

    NAMIBIA

    Asalin hoton, Ullstein Bild / Getty Images

    Shugabar Namibiya ta bayyana ranar tunawa da kisan kiyashi ta farko a ƙasar a matsayin wani muhimmin mataki na tunkarar abubuwan da suka faru ta hanyar yin waiwaye da irin wahalhalun da mutane suka sha a lokacin mulkin mallaka na Jamus.

    Fiye da ƙarni guda da ya gabata, masu mamaya daga Jamus sun kashe sama da mutum dubu bakwai daga al'umomin Oveherero da Nama.

    Shugabar Namibiya ta kunna kyandir domin tunawa da waɗanda kisan kiyashin ya shafa inda kuma ta nanata kira ga Jamus da ta biya diyya.

    Shekaru huɗu da suka gabata ne Jamus ta nemi afuwa saboda rawar da ta taka a abin da ta tabbatar kisan kiyashi ne inda kuma ta yi tayin bayar da sama da dala biliyan ɗaya.

  3. Kotu ta ɗaure Murja Kunya wata shida

    MURJA KUNYA

    Asalin hoton, fb/Murja Kunya

    Wata kotun tarayya da ke zama a Kano ta ɗaure matashiyar nan ƴar TikTok, Murja Kunya tsawon wata shida a gidan yari, bayan samun ta da laifin cin tozarta takardar kuɗi ta naira.

    Alƙalin kotun mai shari'a Simone Amobeda ya ce kotun ta kama Murja da laifin watsa takardar naira da kuma taka ta, a wani lokaci cikin watan Disamban bara, laifin da ya karya tanadin sashi na 21 ƙaramin sashi na ɗaya na dokar nannam namkin Najeriya.

    Kotun ta yankewa Murja Kunya hukuncin zaman gidan yari na wata shida, ko kuma zaɓin biyan tarar naira 50,000.

    Kotun ta kuma umarci Murja ta zamo jakadiyar hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC da kuma babban bankin Najeriya CBN, ta hanyar wayar da kan jama'a game da daina cin mutumcin naira.

    Hukumar EFCC ce ta shigar da ƙarar Murja Kunya a bisa zargin cin mutumcin naira.

    Murja na ɗaya daga cikin matasa masu yawan mabiya a shafin TikTok, sai dai hukumomi a jihar Kano da ke arewacin Najeriya sun sha kama ta bisa laifin yaɗa abubuwan da suka saɓa wa tarbiyya da kuma al'ada.

  4. 'Isra'ila ta kashe ƙanin shugaban Hamas, Mohammed Sinwar"

    YAHAYA SINWAR

    Asalin hoton, IDF

    Firaministan sra'ila Benjamin Natanyahu ya ce an kashe Mohammed Sinwar, ɗaya daga cikin jagororin Hamas da ake nema ruwa a jallo.

    Ɗan'uwansa Yahaya Sinwar shi ne tsohon shugaban ƙungiyar Hamas a Gaza wanda aka kashe a bara a wata fafatawa tsakanin Hamas da sojojin Isra'ila.

    Ana dai kallon Mohammaed Sinwar a matsayin wanda zai gaji yayansa, kuma yana cikin na gaba-gaba da Isra'ila ke nema lokacin da ta kai wani hari a asibitin kudancin Gaza a farkon wannan wata.

    Har yanzu ƙungiyar Hamas ba ta tabbatar da kisan nasa ba.

  5. Hotunan yadda ake taron cikar ECOWAS shekara 50 da kafuwa

    ECOWAS

    Asalin hoton, Presidency

    Bayanan hoto, Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da tsohon shugaban ƙasar, Yakubu Gowon da kuma shugaban hukumar gudanarwar ECOWAS, Umar Alieu Touray a wajen bikin cika shekara 50 da kafa ECOWAS da ke gudana a Lagos.

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu da sauran shugabannin ƙasashen Yammacin Afirka sun hallara a birnin Legas domin bikin cikar ƙungiyar Ecowas shekara 50 da kafuwa.

    Tsohon shugaban mulkin soji na Najeriya Yakubu Gowon, wanda shi ne kaɗai ke raye a cikin shugabannin ƙasa da suka sanya hannu kan dokar da ta kafa ƙungiyar na cikin mahalarta taron.

    Sauran mahalartan sun haɗa da shugaban Laberiya Joseph Boakai, da na Togo Faure Gnassingbé Eyadéma da na Guinea-Bissau Umaro Sissoco Embalo.

    ECOWAS

    Asalin hoton, Presidency

    Bayanan hoto, Shugaban Liberia, Joseph Nyuma Boakai da shugaban Togo, Jean-Lucien Savi de Tové da shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu da tsohon shugaban Najeriya, Yakubu Gowon da shugaban hukumar gudanarwar ECOWAS, Umar Alieu Touray da shugaban jamhuriyar Guinea Bissau, Umaro Sissoco Emalo da sauran shugabanni a wajen bikin cika shekara 50 da kafa ECOWAS da ke gudana a Lagos.
    ECOWAS

    Asalin hoton, Presicency

    Bayanan hoto, Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu da tsohon shugaban Najeriya, Yakubu Gowon a wajen bikin cika shekara 50 da kafa ECOWAS da ke gudana a Lagos.
    ECOWAS

    Asalin hoton, Presidency

    Bayanan hoto, Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu yana sanya hannu a kan katin bikin cika shekara 50 da kafa ECOWAS a zauren taron da aka yi bikin kafa ungiyar a shekarar 1975.
    ECOWAS

    Asalin hoton, Presidency

    Bayanan hoto, Shugaban Liberia, Joseph Nyuma Boakai da shugaban Togo, Jean-Lucien Savi de Tové da shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu da tsohon shugaban Najeriya, Yakubu Gowon da shugaban jamhuriyar Guinea Bissau, Umaro Sissoco Emalo da shugaban hukumar gudanarwar ECOWAS, Umar Alieu Touray da kuma sauran shugabanni suna yanka kek a wajen bikin cika shekara 50 da kafa ECOWAS da ke gudana a Lagos.
  6. Talauci da tashin farashi sun addabi talakan Najeriya - Buhari

    BUHARI

    Asalin hoton, Bashir Ahmad/Twitter

    Bayanan hoto, .

    Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya taya shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu murnar cikar shekara biyu a kan karagar mulkin ƙasar.

    A cikin wani saƙo da mai magana da yawun tsohon shugaban ƙasar Malam Garba Shehu ya fitar, da kuma ke ɗauke da sa hannunsa, Muhammadu Buhari ya roƙi al'umma da su ci gaba da ba gwamnatin jam'iyyar APC cikakken goyon baya.

    Ya ce a daidai lokacin da jam'iyyarsu da kuma gwamnatin ke wannan bikin, ya dace 'yan Najeriya su san da cewa tsarin shugabanci abu ne da ke ci gaba da gudana.

    Ya kuma ce sannu a hankali za a cimma nasara a sabbin tsare-tsaren gwamnati mai ci, idan an saka haƙuri domin ba abu ne da za cimma a dare ɗaya ba.

    Kazalika, Buhari ya ce bai kamata a siyasantar da wasu manufofin da ɗaukar su ya zama wajibi ba.

    Ya ce yana goyo bayan ƙoƙarin da gwamnatin APC ke yi na rage talauci da tashin farashi, da ya ce sun yi matuƙar shafar rayuwar talakawa.

    Tsohon shugaban Najeriyan ya ƙara da cewa matakan da ake ɗauka na rage talauci da tsadar rayuwa, ba abubuwa ne da ya kamata a bar gwamnati ita kaɗai da yin su ba.

    Ya kuma buƙaci 'yan ƙasar da kada su karaya a kan makomar Najeriya

    "Ɓangarori masu zaman kansu da dukan mu 'yan Najeriya ya zama wajibi mu haɗa hannu domin bayar da gudummuwarmu,” in ji tsohon shugaban Najeriyar, Muhammadu Buhari.

  7. Lokuta takwas da shugaba Tinubu ya ciyo bashi a shekaru biyu na mulkinsa

    Tinubu

    Asalin hoton, Bayo/X

    Ƴan Najeriya na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu dangane da buƙatar shugaban ƙasar, Bola Ahmed Tinubu ta neman majalisar dokokin ƙasar su sahhale masa ciyo bashin dala biliyan 21.5 daga ƙasashen waje da kuma lamunin naira biliyan 758 daga cikin gida.

    A wasiƙar da aka karanta a zauren majalisa dattawa, shugaba Tinubu ya ce za a yi amfani da bashin ne domin samar da manyan ayyuka da suka jiɓanci lafiya da ilimi da samar da ruwan sha da kuma biyan basukan da ƴan fansho ke bi.

    Tuni dai aka miƙa buƙatar ga kwamitin majalisar dattawa da ke lura da harkokin basukan gida da na waje domin tantancewa kuma ana sa ran kwamitin zai kammala aikinsa cikin makonni biyu.

    BBC ta yi nazarcin shafukan Bankin Duniya da jaridu tare da sauraron tattaunawar da Sanata Ali Ndume ya yi da gidan talbijin na Arise TV domin zaƙulo lokutan da shugaba Tinubu ya ciyo bashi a shekarun mulkinsa biyu, kamar haka: Ku karanta cikakken labarin

  8. 'Hare-haren Isra'ila a Gaza sun wuce abun da ake buƙata wajen yaƙar Hamas'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Babbar jami’ar diflomasiyyar Tarayyar Turai, Kaja Kallas, ta bayyana cewa hare-haren da Isra’ila ke kai wa a Gaza sun wuce abun da suke buƙata wajen yaƙar Hamas, a yayin da adadin wadanda suka mutu ke ci gaba da ƙaruwa.

    Kallas ta kuma ce Tarayyar Turai ba ta goyon bayan sabon tsarin raba agajin jin kai da Amurka da Isra’ila ke kokarin aiwatarwa wanda ke kaucewa hadin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya da sauran ƙungiyoyin agaji.

    Tun bayan da Isra’ila ta dawo da yaƙi a watan Maris bayan wata yarjejeniyar tsagaita wuta, kimanin mutum 3,924 ne suka mutu a cewar ma’aikatar lafiyar Hamas a Gaza.

    Isra’ila dai ta ci gaba da cewa tana kai hare-haren ne don kawar da Hamas da ceto fursunonin da ƙungiyar ke riƙe da su.

    Sai dai hare-haren kwanan nan sun yi sanadin mutuwar fararen hula da dama.

    Jawabin Kallas ya biyo bayan shiga tsakani da sabon Firaministan Jamus, Friedrich Merz, ya yi, inda ya bayyana cewa “a yanzu ba ya fahimtar manufar Isra’ila a Gaza.”

    Isra’ila dai ta fara kai farmaki a Gaza ne bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga Oktoban 2023, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane aƙalla 1,200 da kuma sace wasu 251.

    A cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza, mutane aƙalla 54,084 ne suka mutu tun daga lokacin.

  9. An sami sabbin hare-haren jirage marasa matuƙa a Sudan

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Rahotanni daga cikin ƙasar Sudan sun bayyana cewa an kai jerin hare-haren jirage mara matuƙa a sassa daban-daban na Sudaƙasar, ciki har da sabbin hare-hare a birnin gaɓar teku na Port Sudan.

    Dakarun RSF in ji rahotan sun kai harin ne jiya a wurare da dama na Port Sudan — birnin da sojojin ƙasar suka ayyana a matsayin babban birninsu na na ɗan wani lokaci, wanda kuma bai fuskanci rikici sosai ba har zuwa farkon wannan watan.

    Hare-haren sun kuma bazu zuwa garin Kosti da kuma yankin Raha Abu Dakna da ke cikin jihar Kordofan na Arewa.

    Sojojin ƙasar dai sun zargi Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) da samar da makamai ga dakarun RSF, zargin da UAE ta musanta.

    A makon da ya gabata, Amurka ta sanar da ƙaƙaba sabbin takunkumi kan sojojin Sudan (SAF), tana mai cewa tana da hujjoji da ke nuna cewa sojojin sun yi amfani da makamai masu guba a yakin da ya kwashe shekaru biyu yana gudana.

  10. Wata ƴar Najeriya ta haihu a lokacin aikin hajji a Madina

    ...

    Asalin hoton, Independent Hajj Reporters of Nigeria/Facebook

    Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar Zamfara ta haihu a birnin Madina ta Saudiyya, yayin da ake shirin gudanar da aikin Hajjin 2025.

    Dandalin ƴan jarida da ke ɗauko rahotannin aikin hajji ne ya wallafa hakan a shafin sada zumutarsa na Facebook.

    Rahoton ya bayyana cewa, bisa ƙa’idojin Hukumar Hajji ta Najeriya (NAHCON), ana hana mata masu juna biyu, musamman waɗanda suka kusan haihuwa tafiya aikin Hajji.

    "Wannan mataki yana da nufin kare lafiyarsu da kuma kauce wa matsalolin da ka iya hana mata masu juna biyu gudanar da ibadar yadda ya kamata." in ji rahoton.

    Likitoci da hukumomin hajji na ganin cewa renon jariri na iya hana mace maida hankali da ƙarfi wajen gudanar da dukan ibadu na aikin Hajji.

  11. Birtaniya ta ɗage takunkumin da ta ƙaƙaba wa manyan jami’an Zimbabwe

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Gwamnatin Birtaniya ta sanar da ɗage takunkumin da ta ƙaƙaba wa wasu manyan jami’an gwamnatin Zimbabwe a matsayin wani mataki na kyautata ɗangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

    Ma’aikatar harkokin waje ta Birtaniya ta bayyana cewa za ta ɗage takunkumin da ke kan mutum huɗu da kuma kamfanin ƙera makamai mallakar gwamnati a Zimbabwe.

    Wannan matakin ya zo watanni bayan Tarayyar Turai ita ma ta sassauta nata takunkumin kan Zimbabwe.

    Birtaniya ta saka takunkumin ne a da saboda damuwa da take haƙƙin ɗan Adam da aka riƙa samu a ƙasar Zimbabwe.

    Masu ruwa da tsaki a Birtaniya da EU na fatan wannan sassauci zai ƙarfafa ci gaba da gyaran siyasa a Zimbabwe.

  12. Ana taron cikar ECOWAS shekara 50 da kafuwa

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugabannin ƙasashe mambobin Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afrika wato ECOWAS na gudanar da taro a ranar Laraban nan a Najeriya domin bikin cikar ƙungiyar shekara 50 da kafuwa.

    Shugabanni da jami’an gwamnati daga ƙasashe 12 na Yammacin Afrika ne suke halartar bikin da ake gudanarwa a birnin Lagos, ƙarkashin jagorancin shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu.

    Wannan bikin na zuwa ne a daidai lokacin da ake tambaya kan makomar ƙungiyar ECOWAS ɗin bayan ficewar wasu ƙasashen yankin Sahel da sojoji ke mulki sakamakon juyin mulki da suka yi.

  13. Kotu ta nemi El-Rufai ya biya diyyar miliyan 900 kan tsare wasu dattawa

    ...

    Asalin hoton, El-Rufai/Facebook

    Wata babbar kotun tarayya da ke Kaduna ta yanke hukunci inda ta nemi tsohon gwamnan Jihar, Nasir El-Rufai, da wasu mutum biyar su biya diyyar naira miliyan 900 a matsayin diyyar tsare wasu dattawan Adara da ke ƙaramar hukuma Kajuru a jihar ba bisa ƙa’ida ba a shekarar 2019 a ƙaramar hukumar Kajuru.

    Gidan talbijin na Channels wanda ya rawaito labarin ya ce mai shari’a Hauwa’u Buhari ce ta yanke hukuncin a kan ƙarar da Awemi Dio Maisamari da wasu dattawan Adara takwas suka shigar, inda kotu ta tabbatar da cewa an tsare su ne bisa zargin hannu a kisan sarkin gargajiyarsu, Raphael Maiwada Galadima, ba tare da wani dalilin doka ba.

    Kotu ta ce El-Rufai ya ci gaba da matsa lamba a kan a kama su, kuma ya aikata hakan ne ba a matsayinsa na gwamna ba.

    Kotu ta yi watsi da korafe-korafen da waɗanda ake ƙara suka gabatar.

    Lauyar da ta wakilci masu ƙarar, Gloria Ballason, ta bayyana hukuncin a matsayin babbar nasara a yaƙi da cin zarafin da gwamnoni da shugabanni ke yi da amfani da karfi da ikon da ke hannunsu.

    Dattawan takwas, ciki har da tsohon kwamishina na ƴan sanda mai ritaya, an kama su ne a wani taron al'umma da El-Rufai ya shirya a shekarar 2019, bayan sace da kashe sarkinsu.

  14. Ƙungiyar AES da Rasha za su kafa tsarin shari'a na bai ɗaya

    ...

    Asalin hoton, Burkina Faso Presidency

    Ministan shari’a na Mali, Mamadou Kassogué, ya bayyana cewa ƙungiyar ƙasashen Sahel (AES) tare da Rasha na shirin kafa tsarin shari'ah na bai ɗaya da zai inganta haɗin gwiwa a fannin shari’a.

    Ƙungiyar AES ɗin ta ƙunshi Mali da Burkina Faso da Nijar – kasashe uku da sojoji ke mulki kuma suna da ƙarfi a dangantakarsu da Rasha.

    Kassogué, wanda ke magana daga Rasha, ya ce kowace ƙasa za ta naɗa wakili ko mai kula da sha’anin hadin gwiwa domin ƙara karfafa alaka.

    Ya ƙara da cewa ana duba yiwuwar samar da rumbun bayanai na hadin gwiwa kan laifuka, wanda zai ba da damar musayar ilimi da ƙwarewa.

    Shugabannin wadannan ƙasashen da sojoji ke jagoranta suna halartar taron tsaro tsakanin Rasha da kasashen yankin Sahel da ake gudanarwa a birnin Moscow.

  15. Hukumar kwastam ta Najeriya ta kama mota ɗauke da sinadaran haɗa bam

    ...

    Asalin hoton, Nigeria custom service/Facebook

    Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen yankin Seme, ta kama wata mota da ake zargin tana ɗauke da kayan haɗa bam (IED).

    Wannan na ƙunshe ne a wani bidiyo da hukumar ta wallafa a shafinta na X, inda jami’anta ke binciken motar da aka kama a kan titin Lagos zuwa Badagry.

    An gano cikin motar akwai kwanso guda shida na ma'adani mai launin azurfa mai ɗauke da guba mai ƙarfi da aka fi sani da corrosive mercury — wanda ake kyautata zaton ana amfani da shi wajen haɗa abubuwan fashewa.

    Shugaban Kwastam na yankin, Kwanturola Ben Oramalugu, ya ce an kama mutum ɗaya da ake zargin yana da alaƙa da motar.

    Ya bayyana cewa nasarar kama motar na nuna yadda Kwastam ke cikin shiri da kulawa wajen kare tsaron kasa.

    Oramalugu ya kara da cewa wannan aiki na cikin matakan da Kwastam ke dauka don dakile ayyukan fasa-kwauri da sauran laifuka a iyakokin Najeriya.

    Baya ga motar da ake zargin tana ɗauke da kayan haɗa bam, hukumar ta kuma kama wasu kayayyaki da dama da suka saɓa wa doka.

    Kayayyakin sun hada da kuɗaɗen ƙasashen waje daga Birtaniya da Kanada, da Amurka da darajarsu ta kai kusan naira miliyan tara, wanda hakan ya saɓa dokar harajin kaya na waje.

    Sauran kayayyakin da aka kama sun hada da robar ganyen wiwi guda 553 da buhunan shinkafar waje 1,415 da jarkokin man fetur guda 750, da kuma magungunan da ba a yi rijistarsu ba.

    Kwanturola Oramalugu ya ce hukumar za ta miƙa kayayyakin da aka kama ga hukumomin da suka dace domin gudanar da bincike tare da ɗaukar mataki, da gurfanar da wadanda ake zargi.

  16. Namibia na alhinin kisan ƴan ƙasar dubu 70 da Jamus tayi sama da shekaru 100

    ...

    Asalin hoton, Ullstein Bild / Getty Images

    A ranar Laraban nan ne ƙasar Namibia ke taron juyayin tuna kisan gilla da sojijin Jamus su ka yi wa ƴan ƙasar dubu 70, a zaman turawan mulki mallaka sama da shekaru 100 da suka gabata.

    A shekaru huɗu da suka gabata ne Jamus ta nemi afuwan rawar da ta taka wajen kisan dubban mutanen da suka fito daga ƙabilar Ovaherero da Nama, wadda tace ta yarda an aikata kisan ƙare dangi a kansu.

    Shekaru 40 kafin kisan kiyashin da aka yi wa ƴan Namibia ɗin, an rinƙa amfani da mutanen wajen gudanar da gwaji ta hanyar azabarta da kisa kan 'yan Afirka a sansanoni sojojin Jamus.

    An azabtar tare da kashe mutanen ne saboda turjiya da ƙin yarda da Turawa su ƙwace musu filaye da dabobbi.

  17. Amurka za ta dakatar da bai wa ɗalibai bizar shiga ƙasar

    ...

    Gwamnatin shugaban Amurka, Donald Trump ta umarci ofisoshin jakadancinta da ke faɗin duniya su dakatar da bai wa ɗalibai da sauran mutane da ke neman bizar ziyara zuwa ƙasar.

    Gwamnatin ta ba da umarnin ne yayin da take faɗaɗa shirin binciken bada bisa ta hanyar tantace abubuwan da mutum ke wallafawa a shafukan sada zumunta, musamma ɗalibai.

    Wasu daliban kuma da tuni suke Amurka an kwace bizarsu saboda shiga gangamin nuna goyon-bayan Falasdinawa.

    Wannan na daga cikin matakan da Trump ke ɗauka na hana manyan makarantun Amurka da suka yi fice wajen dogaro da kuɗaden makaranta da suke samu daga ɗaliban ketare.

    Kafin wannan lokaci fadar gwamnatin Amurka White House ta ce gwamnatin Trump ta buƙaci dukkanin ma'aikatun Amurka su datse tallafin da suke bai wa jami'ar Havard da suke amfani da shi wajen bada tallafin karatu.

  18. Assalamu Alaikum

    Masu bibiyar labaran BBC Hausa kai tsaye barkan mu da hantsin Laraba.

    Fatan kun tashi lafiya.

    Kamar kullum yau ma ku kasance da mu domin samun labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da kuma sauran sassan duniya.