window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 13/04/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 13/04/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Ma'aikacin jinyar da ya ɓace a watan jiya a Gaza yana Isra'ila - Red Cross

    Ƙungiyar agaji ta Red Cross ta ce, ma'aikacin lafiyar nan Bafalasdɗne - wanda ya ɓace tun bayan wani hari da Isra'ila ta kai a Gaza a watan da ya wuce - wanda a lokacin ma'aikatan agaji goma sha biyar (15) suka mutu, yana tsare a hannun hukumomin Isra'ila.

    Ƙungiyar ta ce, an ba ta damar ganin ma'aikacin na ƙungiyar, Assad al-Nsasrah, wanda ba a san halin da yake ciki ba kafin yanzu.

    Sai dai hukumomin sojin Isra'ila ba su tabbatar da labarin ma.

    An gano gawarwakin ma'aikatan agajin 15 binne a wani ƙaton kabari na bai-ɗaya a kudancin Gaza a watan Maris.

    Majalisar Ɗinkin Duniya da kuma ƙungiyar ta Red Crescent sun zargi sojojin Isra'ila da kashe ma'aikatan a lokacin da suka kai ɗauki.

  2. Dakarun RSF sun ce sun ƙwace iko da sansanin ƴangudun hijira na Zamzam na Sudan

    RSF

    Asalin hoton, Getty Images

    Dakarun ƙungiyar RSF da ke yaƙi da rundunar sojin Sudan sun ce sun ƙwace iko da sansanin ƴangudun hijira na Zamzam, da ke yankin yammacin Darfur.

    A wata sanarwa da RSF ɗin ta fitar, ta ce ta tura mayaƙanta domin kare farar hula da ma'aikatan agaji.

    Wakiliyar BBC ta ce, labarin harin ya bayyana ne a jajiberin shekara biyu da fara yaƙin basasar.

    Rahotanni sun ce mayaƙan RSF ɗin sun shafe kwanaki suna ruwan makamai ta sama a yaƙin da suke yi da gwamnatin ƙasar ta Sudan.

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce ta damu matuƙa gaya da kisan farar hula sama da 100 - da suka haɗa da ma'aikatan jinƙai tara a yankin.

  3. Soyinka ya soki gwamnati kan haramta waƙar Eedris Abdulkareem

    Eedris Abdulkareem

    Asalin hoton, Eedris Abdulkareem

    Fitaccen marubucin Najeriya, wanda ya samu lambar yabo ta Nobel, Farfesa Wole Soyinka ya soki Hukumar Kula da Kafofin Sadarwa ta Najeriya bisa haramta waƙar Eadris Abdulkareem, wadda aka soki gwamnatin Tinubu a cikinta.

    Soyinka ya bayyana matakin a matsayin komawa gidan jiya wajen tantance ayyukan fasaha, da kuma yin barazana ga ƴancin tofa albarkacin baki.

    A wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi, marubucin ya ce, "ta wajen wani mai aikin fasahar zane-zane ne na samu labarin abin ake ciki, inda na fahimci cewa an fara komawa gidan jiya wajen tace ayyukan fasaha ta hanyar haramta waƙar nan ta Eadris Abdulkareem,” kamar yadda Soyinka ya bayyana a wata sanarwa da PM news ta ruwaito.

    Da yake yin shaguɓe kan matakin na gwamnatin ƙasar, Soyinka ya ce ba waƙar kaɗai ya kamata a haramta ba, "tunda haka ne sai a kama tare da hukunta mawaƙin shi ma, sannan a haramta ƙungiyar PMAN da ma duk wata ƙungiya da Abdulkareem yake ciki."

    Sai dai Soyinka ya ce duk da cewa bai saurari waƙar ba, "irin wannan haramcin ba abin da yake ƙarawa sai ɗaukaka ga mawaƙi."

  4. Gwamnatin Najeriya ta yi martani kan umarnin kotun Amurka na fitar da bayanan zargin Tinubu da safarar ƙwayoyi

    Tinubu

    Asalin hoton, OTHERS

    Fadar Gwamnatin Najeriya ta yi martani kan umarnin da wani alƙali a wata kotun Amurka da ke zamanta a birnin Washigngton DC ya bayar, inda ya buƙaci a fitar da bayanan zargin Tinubu da safarar ƙwayoyi.

    A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce wannan ba sabon ba ne.

    Ya ce, "ƴanjarida suna ta neman jin ta bakin fadar shugaban Najeriya kan hukuncin alƙalin kotun Amurka da ke Washington, inda ya buƙaci FBI da DEA su fitar da sakamakon binciken da aka yi wa Bola Tinubu kan zarginsa da safarar miyagun ƙwayoyi.

    "Amsarmu ita ce babu wani sabon abu a hukuncin. Sakamakon bincike ya daɗe da fita, domin rahoton binciken FBI da DEA sun fi shekara 30 a fili. Rahoton bai nuna shugaban Najeriya yana da laifi ba."

  5. 'Harin Rasha ya kashe aƙalla mutum 32 a Ukraine'

    Ukraine

    Asalin hoton, State Emergency Service of Ukraine

    Aƙalla mutum 32 ne suka mutu, sannan wasu 84 suka jikkata, ciki har da ƙananan yara a wani hari da Rasha ta kai a garin Sumy a yau Lahadi, kamar yadda hukumomin Ukraine suka bayyana.

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce "hare-hare ne na rashin tausayi na makamai masu linzami da Rasha ta yi domin kashe mutanen da babu ruwansu," sannan ya ƙara da cewa idan ba a dakatar da Rasha ba, "za ta cigaba da jan yaƙin ne."

    Makamai masu linzami samfurin Iskander guda biyu ne aka harba a yankin da misalin ƙarfe 10:15, inda suka sauka a kusa da Jami'ar Jihar da majalisar jihar.

    Hukumomi a Ukraine sun shaida wa BBC cewa harin ya tarwatsa aƙalla gidaje guda 20, ciki har da cibiyoyin karatu guda huɗu da shaguna da gidaje da motoci guda goma da sauransu.

    Zelensky ya yi kira ga ƙsashe da su ɗauki mataki "mai tsauri" kan Rasha, inda ya ce "tattaunawar da ake yi ba ta taɓa hana Rasha kai hare-hare ba."

    "Amurka da tarayyar turai da ma duk wata ƙasa na so a kawo ƙarshen wannan yaƙin da kisan gilla, amma Rasha tana so ta cigaba. Idan ba an takura mata ba, lallai ba za a samu zaman lafiya ba," in ji shi.

    Ministan harkokin wajen Ukraine Andriy Sybiha ya yi Allah wadai da harin, wanda a cewarsa, "an kashe fararen hula da dama. Kai irin wannan harin a ranar da kiristoci suke taruwa domin ibada (Lahadi) ba ƙaramin shaiɗanci ba ne," in ji shi kamar yadda ya rubuta a shafinsa na X.

  6. Shugaban mulkin soji na Gabon, Brice Nguema ya lashe zaben shugaban kasar

    Gabon

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakamakon wucin-gadi na zaɓen shugaban ƙasar Gabon ya nuna cewa shugaban riƙo kuma jagoran juyin mulkin ƙasar, Brice Oligui Nguema ne ya lashe zaɓen da kashi 90.35 na ƙuri'u da aka kaɗa, kamar yadda ma'aikatar harkokin cikin gida na ƙasar ta bayyana.

    Da wannan sakamakon, Nguema zai cigaba da zama shugabantar ƙasar bayan shekara biyu yana jagorancinta bayan juyin mulkin da ya hamɓarar da Ali Bongo.

    "Mr Brice Clotaire Oligui Nguema ya lashe zaɓen shugaban ƙasar bayan samun ƙuri'u mafi rinjaye, inda ya samu ƙuri'a 575,222," in ji ministan harkokin wajen ƙasar, Hermann Immongault.

    Wanda ke biye masa shi ne Alain Claude Billie-by-Nze, wanda ya samu kashi 3.02 na ƙuri'un da aka kaɗa.

    Wakilin BBC ya ce, Nguema, ya ce zai kasance shugaba ga dukkanin ƴan ƙasar ta Gabon ba tare da wani bambance ba.

    Zaɓen shi ne na farko, tun bayan da sojoji suka hamɓarar da gwamnatin iyalan gidan Bongo da suka shafe sama da shekara 50 suna mulkin ƙasar ta yankin tsakiyar Afirka.

    Bayanai sun nuna cewa an samu fitar jama'a sama da kashi saba'in cikin ɗari kuma zaɓen ya kawo ƙarshen mulkin sojin ke nan.

    Dama dai tun kafin zaɓen ake hasashen jagoran gwamnatin sojin ne zai lashe zaɓen, inda masu sukar yanayin zaɓen suke cewa an tsara zaɓen ne ta yadda zai sauƙaƙa masa samun nasara.

  7. Ta yaya mace za ta mori rayuwar jima'i a shekarun ɗaukewar jinin al'ada?

    Jima

    Asalin hoton, Getty Images

    Raguwar sha'awa da bushewar gaba da kuma jin zafi a lokacin saduwa, waɗannan wasu ne daga cikin alamomin da mata ke fuskanta a lokacin da suka daina jinin al'ada.

    Da dama cikin mata sauye-sauyen kan fara ne tsawo shekara 10 gabanin daina al'adar, wani lokaci da ake kira alamar kusantar lokacin daina haihuwa.

    Suzan mai shekara 40 da ɗoriya da ke zaune a Vancouver a ƙasar Canada - wadda a yanzu haka ke cikin wannan lokaci - ta ce tana jin zafi a lokacin saduwa.

  8. Iran ta yi Allah wadai ta kisan ƴan Pakistan takwas a ƙasarta

    Iran ta yi Allah wadai da kakkausar murya kan kisan wasu ma'aikatan Pakistan takwas a kudu maso gabashin ƙasar Iran a ranar Asabar.

    Ƙungiyar ƴan awaren Balochistan National Army da ke Pakistan ta ce ita ta kai harin kan mutanen waɗanda ke zaune a garejin gyaran mota a lardin Sistan-Baluchestan.

    Ofishin jakadancin Iran a birnin Islamabad ya bayyana harin da rashin imani tare da yin kira ga ƙasashen yankin su haɗa kai wajen martani.

    Yayin da yake bayyana damuwarsa kan harin, Firmaministan Pakistan, Muhammad Shehbaz Sharif, ya yi kiran samar da haɗin kan ƙasashen yankin Gabas ta Tsakiya domin kawar da abin da ya kira ayyukan ta'addanci.

  9. Amurka za ta taimaka wa Saudiyya don samar mata makamashin nukiliya

    Sbuwar tashar makamashin nukiliya

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakataren makamashi na Amurka ya ce ƙasarsa da kuma Saudiyya na kan hanyar cimma yarjejeniyar aiki tare domin samar wa Saudiyyar makamashin Nukiliya.

    Chris Wright ya bayyana haka ne a birnin Riyadh lokacin da yake jawabi bayan ganawa da takwaransa na Saudiyya, gabanin ziyarar Shugaba Trump da aka shirya zuwa Saudiyya a watan gobe.

    A lokacin gwamnatin Biden ne aka fara tattauna yarjejeniyar, a wani mataki da ake ganin zai sa Saudiyya ta kyautata alaƙa da Isra'ila.

    Babban abin da ke kawo cikas shi ne yadda Saudiyya ta ƙi sanya hannu kan yarjejeniyar da za ta kawar da yiwuwar inganta sinadarin Uranium.

  10. China ta yi maraba da matakin Amurka na cire haraji kan wasu kayan laturoni

    kayan lturoni

    Asalin hoton, Getty Images

    China ta yi maraba da matakin Amurka na cire haraji kan wasu kayan laturoni, tana mai bayyana hakan da matakin farko na gyara abin da ta ce kuskuren saka wa kayyakin China harajin kashi 145.

    A ranar Juma'a ne Amurka ta bayyana cire haraji kan wayoyin hannu da kwamfutoci da kuma wasu ƙananan kayan laturoni.

    Matakin ya taimaka wa kamfanonin fasaha na Amurka da masu lura da sarrafa kayyaki, waɗanda da yawansu ke kudancin China.

    Ma'aikatar kasuwancin China ta nanata kiranta ga Amurka ta jingine duka haraje-harajen da ta ƙara, kodayake ba ta yi magana kan ƙarin harajin da ƙasar ta ƙaƙaba wa kayyakin Amurka ba.

  11. Ƴancirani sun kafa tarihin shiga Birtaniya a kwana guda

    Baƙin haure

    Asalin hoton, Getty Images

    Yancirani sun kafa tarihin shiga Birtaniya a kwana guda, bayan da ƴancirani marasa takardun izini suka shiga ƙasar a ƙananan jiragen ruwa daga Faransa.

    Ƴancirani 656 ne suka tsallaka ƙasar cikin ƙananan jiragen ruwa 11 a ranar Asabar, adadi da ya zarta na rana guda da aka taɓa gani a farkon watan da ya gabata.

    Adadin ya sa adadin baƙin hauren da suka shiga Birtaniya a shekarar nan ya zarta 8,000, adadin da ya ƙaru da kusan rabi idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata daidai wannan lokacin.

  12. Ana ci gaba da kai hare-hare kan sansanonin ƴangudun hijira a Sudan

    Mazauna sansanin ƴan gudun hijira da ke Zamzam a Sudan sun shaida wa BBC cewa ana ci gaba da harbe-harbe a sansanin bayan harin mayaƙan RSF.

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta kaɗu da kashe-kashen baya-bayan da aka samua ƙasar na fiye da fararen 100, ciki har da ma'aikatan agaji tara a yammacin yankin Darfur - wanda aka ɗora alhakinsa kan mayaƙan RSF mai yaƙi da dakarun ƙasar.

    Majalisar ta ce kashe-kashen a sansanonin biyu da kuma birnin El Fasher ya haifar da yawaitar hare-hare kan ƴan gudun hijira da ma'aikatan agaji.

  13. United ta bai wa Onana hutu a wasan da Newcastle

    Andre Onana

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Cikin wasa 43 da ɗan wasan ya buga a kakar bana, sau 10 ne kawai ƙwallo ba ta shiga ragarsa ba.

    Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester United ta ajiye mai tsaron ragarta, Andre Onana a wasan da ƙungiyar za ta kara da Newcastle a gasar Premier League a yau Lahadi.

    Onana ya tafka kura-kurai da suka janyo ƙungiyarsa buga kunnen doki, 2-2 a gasar Zakarun Turai ta Europa, kwana guda bayan tsohon ɗan wasan ƙungiyar, Nemanja Matic ya bayyana shi da ''ɗaya daga cikin masu tsaron raga marasa inganci''.

    Wasu majiyoyi daga ƙungiyar sun ce an cire Onana daga tawagar ne domin ''ba shi damar hutawa don dawo da ƙarsashinsa''.

    Ana sa ran ɗan wasan zai fuskanci ƙalubalen saka shi cikin tawagar da za ta kara da Lyon a wasan kwata fayinal na gasar Zakarun Turai ta Europa a ranar Alhamis.

  14. Saudiyya ta ce masu bizar aikin hajji ne kawai za ta bari su shiga ƙasar daga 29 ga Afrilu

    Mahajjata

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasar Saudiyya ta ce daga ranar 29 ga watan Afrilun da muke ciki ba wanda za ta bari ya shiga ƙasar sai mai ɗauke da bizar aikin hajji.

    Jaridar Saudi Gazzet ta ambato ma'aikatar cikin gida ta ƙasar na bayyana haka cikin sabbin matakan da ta ɗauka kan tsare-tsaren aikin hajjin bana.

    Sabbin matakan sun tanadi cewa za a haramta wa ƴan asalin ƙasar mazauna ƙetare shiga birnin Makka, in ba da wani muhimmin dalili ba.

    Ma'aikatar ta ƙara da cewa za a bai wa asalin ƴan ƙasar izinin shiga birnin Makka ne kawai idan adireshin gidansu ya nuna cewa a birnin suke da zama, ko waɗanda aka bai wa damar yin aiki a harami.

    A cewar ma'aikatar harkokin cikin gidan wannan wani mataki ne manyan sauye-sauye da ta ɓullo da su domin lura da aikin hajjin bana na tabbatar da lafiya da tsaron mahajjata.

    Ma'aikatar ta ƙara da cewa daga ranar 13 ga watan Afrilu, ƙasar za ta daina bayar da biza ga masu zuwa ibadar Umara, yayin da ta saka ranar 29 ga watan Afrilun a matsayin ranar da masu ziyarar Umara daga ƙasashen waje za su fice daga ƙasar, domin bayar da damar shirye-shiryen aikin hajji.

  15. Mutum takwas sun mutu bayan da motarsu ta taka nakiya a Borno

    Zulum

    Asalin hoton, Borno Gov/X

    Mutum takwas sun sun mutu yayin da wasu da dama suka jikkata bayan da wata motar bas ta taka nakiya a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa a ranar Asabar.

    Gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya zargi ƙungiyar Boko Haram da dasa nakiyar a kan babban titi da ya haɗa Maiduguri, babban birnin jihar da kuma garin Damboa.

    A baya rundunar sojin Najeriya ta rufe titin sakamakon ta'azzarar matsalolin tsaro a yankin.

    Daga baya ne gwamnan jihar ya bayar da umarnin buɗe titin inda sojoji ke bai wa matafiya kariya ta hanyar yi musu rakiya.

    To sai dai gwamnan ya ce harin na jiya Asabar ba zai sa a daina bin titin ba.

    "Za mu tabbatar da cewa an ci gaba da zirga-zirga tsakanin Maiduguri zuwa Damboa, wannan hari ba zai hana mu bin titin ba," in ji Gwamna Zulum.

    Dasa nakiyoyi ya kasance ɗaya daga cikin hanyoyin da ƙungiyar Boko Haram ke kai hare-hare. Ko a shekarar da ga gabata ma irin wannan hari ya kashe sojojin ƙasar bakwai, bayan da motarsu ta taka nakiya.

    A baya-bayan nan dai hare-haren Boko Haram na sake dawowa musamman a jihar Borno, lamarin da ya sa gwamnan jihar ya fito ya koka a baya-bayan nan.

  16. Harin Isra'ila a asibitin Gaza ya tarwatsa sashen kula da marasa lafiya na musamman

    Ma'aikatan lafiya a asibiti guda ɗaya tilo da ke aiki a birnin Gaza sun ce harin makami mai linzami da Isra'ila ta kai kan ginin ya lalata sashen bayar da kulawar gaggawa da ɓangaren tiyata na asibitin.

    Isra'ila ta ce ta kai harin ne da nufin tarwatsa cibiyar bayar da umarni ta Hamas.

    Rahotonni sun ce an bai wa hukumomin asibitin Al-Ahli Baptist gargaɗin miti 20 domin ma'aikata da majinyata sun fice. Kawo yanzu ba a samu rahoton rasa rai ba.

    Bidiyon da wasu ƴan gwagwarmaya suka yaɗa sun nuna hayaƙi na tashi, da marasa lafiya da waɗanda suka jikka a lokacin da suke barin asibitin yayin da aka ga gomman Falasɗinawa na barin asibitin inda suke neman mafaka.

    Hamas ta ayyana harin a matsayin ''mummunan laifi''.

  17. Hare-haren RSF sun kashe fiye da mutum 100 a Sudan - MDD

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce an ankarar da ita baya-bayan nan game da kisan sama da farar hula ɗari har da ma'aikatan agaji tara a jihar Darfur da ke Sudan sakamakon hare-hare da dakarun RSF da ke yaƙi da gwamnati suka kai.

    Majalisar ta ce kisan da aka yi a El Fasher da sansanoni biyu, na alamta ta'azzarar munanan hare-hare kan mutanen da suka ɗaiɗaita da kuma jami'an agaji.

    RSF ta musanta aikata miyagun ayyuka a sansanin Zamzam.

    Ƙungiyar agaji ta Charity Relief ta tabbatar da mutuwar ma'aikatanta tara.

    Wani fitaccen ɗan tsere a Sudan Abubakar Kaki na daga cikin mutanen da aka kashe a farmakin da RSF ta kai gidansa da ke El Fasher.

  18. Ana ci gaba da ƙidaya ƙuri'u a zaɓen shugaban ƙasar Gabon

    Gabon

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana ci gaba da ƙidaya ƙuri'u a zaɓen shugaban ƙasar Gabon da aka gudanar a ranar Asabar.

    Wannan ne karon farko da aka yi zaɓe tun bayan da sojoji suka ƙwace mulki shekara biyu da suka gabata bayan da suka hamɓarar da iyalin Bongo da suka shafe fiye da rabin ƙarni suna mulki.

    Bayanai na cewa mutane sun fita zaɓen sosai kusan kashi 87 cikin 100.

    Janar Brice Oligui Nguema - wanda ya jagoranci jyin mulƙin ƙasar a 2023 - ne mutumin da ake tunanin zai lashe zaɓen.

    Abokin karawarsa kuma shi ne tsohon Firaiministan ƙasar da aka tilasta wa yin murabus bayan juyin mulkin.

  19. Sallama

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da hutun ƙarshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci, domin zagawa da ku wasu sassan duniya don jin yadda suka wayi gari.

    Kar ku manta da shafukanmu na sada zumunta domin kallon ƙayatattun bidiyo da hotuna, da ma wasu labaran.