window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 10/01/2025.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Abdullahi Bello Diginza, Isiyaku Muhammed, Usman Minjibir, da Umar Mikail

  1. Lauyoyi sun buƙaci a hukunta wanda ake zargi da ya yi wa ƴar shekara 9 fyaɗe a Jigawa

    Kotu

    Asalin hoton, Getty Images

    A Najeriya wasu ƙungiyoyin lauyoyi da masu kare haƙƙin dan-adam sun yi kira da a kama tare da hukunta wanda ake zargi da hannu a yi wa wata ƙaramar yarinya ƴar shekara 9 fyaɗe a jihar Jigawa.

    A yanzu haka ana ci gaba da jinyar yarinyar a asibiti sakamakon munanan raunukan da aka ji mata.

    Barista Aisha Ali Tijjani, lauya ce mai zaman kanta malama a kwalejin nazarin aikin shari’a ta Aminu Kano da ke jihar Kano, ta yi wa BBC ƙarin bayani kan yadda suke kallon wannan batu ta fuskar shari’a, inda ta ce za su bi kadin lamari.

  2. An tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 10 a gobarar dajin Los Angeles

    Wutar daji

    Asalin hoton, Reuters

    Jami'ai a birnin Los Angeles sun ce mummunar gobarar daji ta lalata sama da gidaje dubu 10 da wasu gine-gine suka a jihar Californian.

    Kawo yanzu adadin waɗanda aka tabbatar da mutuwarsu ya kai 7, ana kuma ci gaba da neman wasu.

    Brad Sherman ɗan majalisa ne mai wakiltar Carlifornia, ya bayyana halin da ake ciki, inda ya ce wannan ce gobara mafi muni a tarihin Amurka.

    Ya ce babu wanda ya taɓa tsammanin lamarin zai kai haka ga kuma iska mai ƙarfin da ake fama da ita na ƙara rura wutar.

    Ƙiyasin ɓarnar da wutar dajin ta yi ya tashi sosai zuwa aƙalla dala miliyan 135.

    An tura jami’an tsaro na ƙasa 400 a yankin domin taimaka wa ƴansanda aikin, bayan da aka samu rahotanni sata ko kwashe kayan jama’a.

    Da yake magana a wani taron manema labarai , babban jami’in ƴansanda na birnin na Los Angeles, Jim McDonnell, ya ce abin da suka mayar da hankali yanzu a kansa shi ne kare aikata miyagun laifuka.

    Ya ce, "kare gidaje da harkokin kasuwanci a wuraren da aka kwashe jama’a da inda babu tsaro sosai shi ne abin da muka bayar da fifiko a kai yanzu, domin tabbatar da ganin cewa babu wanda ya yi amfani da damar mawuyacin halin da ake ciki. Ko kaɗan ba za a lamunta wawashe kayan jama’a ba ko wawason kaya ko ribatar wannan bala’i."

  3. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Juma'a daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sadarwa irin su X da Facebook da Instagram domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo.

    Ku kasance tare da mu.