window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 20/04/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 20/04/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Waɗanda suka rasu a ruftawar benen Legas sun ƙaru zuwa biyar

    Adadin waɗanda suka rasu a ruftawar bene a yankin Ojodu Berger da ke jihar Legas a kudancin Najeriya ya ƙaru zuwa biyar.

    Haka kuma hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya ta ce an ceto ƙarin mutum uku a cikin baraguzan ginin.

    Kodinetan yanki na NEMA mai kula da yankin kudu maso yamma, Ibrahim Farinloye ne ya sanar da haka a safiyar Lahadi, inda ya ce mutum biyar ne suka rasu, amma sun ceto mutum 20 jimilla.

    Farinloye ya ce daga cikin waɗanda aka ceto akwai mata da maza.

    "Sai dai mun ciro gawarwakin mutum biyar - mata uku maza biyu," in ji shi.

  2. Me ke haddasa sanƙo kuma ta yaya za a kauce masa?

    Sanƙo

    Asalin hoton, Getty Images

    Zubewar gashi kan faru da kowa, ba tare da la'akari da jinsi ko shekaru da ƙabila ba.

    Za ka iya fara rasa gashin kanka saboda wasu dalilai masu yawa, da suka haɗa da na gado ko sharain magani ko ma yanayin yadda kake gudanar da rayuwarka.

    Domin gano dalilai da kuma magance sanƙo, mun yi magana da Enitan Agidee, daraktan a wata cibiyar kula da gashi da sanƙo da ke Birtaniya, kuma likitar da ke duba masu lalurar sano musamman mata.

  3. DR Kongo ta haramta wa Joseph Kabila yin taro saboda zargin alaƙarsa da M23

    Joseph Kabila

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Joseph Kabila ya sha musanta alaƙa da ƙungiyar M23

    Jamhuriyar Dimokaɗiyyar Kongo ta haramta wani taron biki da tsohon shugaban ƙasar, Joseph Kabila ya shirya gudanarwa, bayan da gwamnati ta zarge shi da alaƙa da ƙungiyar ƴantawayen M23 - da ta ƙwace wasu manyan yankunan gabashin ƙasar.

    Haramcin na zuwa ne bayan da rahotoni suka ce Kabila ya koma ƙasar bayan shafe shekara biyu a Afirka ta Kudu.

    An ce tsohon shugaban ya sauka a birnin Goma - wanda mayaƙan M23 da ke samun goyon bayan Rwanda suka ƙwace a watan Janairu.

    Mista Kabila ya shugabanci ƙasar na tawon shekara 18, bayan ya gaji mahaifinsa, Laurent wanda aka harbe ya mutu a 2001.

    Cikin wata sanarwa da ma'aikatar cikin gida ta ƙasar ta fitar ta ce an haramta taron ne saboda rashin sanin ''matsayin jam'iyyarsa'' kan ƙwace wasu yankunan ƙasar da M23 ta yi.

    An bayar da rahoton cewa Mista Kabila ya zaɓi ya koma Goma ne saboda a can ne za a kare shi daga abin da jam'iyyarsa ta kira ''maƙiya''.

    Kawo yanzu dai jam'iyyarsa ta PPRD ba ta ce komai ba game da matakin.

  4. Isra'ila ta kori wani mataimakin kwamanda saboda kisan jami'an lafiya a Gaza

    Isra'ila ta ce ta kori wani mataimakin kwamanda a rundunar sojin ƙasar saboda rawar da ya taka a kisan jami'an lafiyar Falasɗinawa 15 a Gaza cikin watan da ya gabata.

    Binciken Isra'ila ya gano jerin kura-kurai, ciki har da saɓa wa umarni da kasa bayyana cikakken rahoton faruwar lamarin.

    Tawagar binciken ta ce waɗanda suka aikata kisan sun buɗe wuta ne kan tawagar bisa tsammanin barazanar mayaƙan Hamas.

    Binciken ya kuma ce shida cikin mutanen da aka kashe mayaƙan Hamas ne.

    Kisan ya haddasa zazzafar suka a faɗin duniya, wani bidiyo da ɗaya daga cikin likitocin ya ɗauka ya nuna tawagar motocin nasu na tafiya cikin dare tare da kunna wutar da ke nuna alamar motocin jami'an lafiya ne, wani abu da ya saɓa wa iƙirarin Isra'ilar na farko.

  5. NDLEA ta gano hodar ibilis da aka so yin safararta zuwa Saudiyya cikin littattafan addini

    HH

    Asalin hoton, NDLEA

    Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA), ta kama wata hodar ibilis da ke ƙunshe cikin wasu littattafn addini da aka so yin safararta zuwa ƙasar Saudiyya.

    Cikin sanarwar nasarorin mako-mako na hukumar da kakakinta, Femi Babafemi ya aike wa BBC ya ce hodar, ƙulli 20 mai nauyin giram 500 an shirya ta cikin shafukan littattafan da nufin safararta zuwa ƙasar ta Saudiyya.

    Ya ce jami'an hukumar ne suka yi nasarar gano hodar ranar 15 ga watan Afrilu a maɗaukan kaya na wani kamfani da ke shirin fitar da kaya zuwa ƙasashen waje.

    Haka Babafemi ya ce hukumar ta kuma gano wata tabar wiwi cikin wani maɗauki da aka shigar da shi ƙasar daga Amurka.

    Hukumar ta kuma kama wani matashi, mai shekara 22 a kan hanyar zuwa Bichi da ke jihar Kano da kwalaben allurar pentazocine 277, manne da silatif a cinyoyinsa da al'aurarsa.

  6. Zaki ya halaka wata yarinya a Kenya

    Zaki

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da gandun dajin Kenya ta tabbatar da cewa zaki ya kashe wata yarinya mai shekara 14 a wajen birnin Nairobi.

    Zakin ya kamo yarinyar ne a wani gida da ke kusa da gandun dajin Nairobi, a cewar hukumar kula da gandun dajin.

    Wani matashi ne ya ankarar da hukumar, inda nan take jami'ai suka bi sawun zakin zuwa kusa da Kogin Mbagathi, inda a nan ne suka gano guntun gangar jikin yarinyar - wadda ƴar furamare ce.

    Ba a dai gano zakin ba, amma hukumar ta ce ta ɗana masa tarko tare da baza jami'ai domin nemansa.

    Hukumar ta ce an ɗuki ƙarin matakan tsaro domin hana zakin sake auka wa wasu mutanen.

    Gidan namun dajin ƙasar mai tazarar kilomita 10 daga tsakiyar birnin Nairobi, ya kasance gida ga manyan namun daji irin su zakuna da raƙuman dawa da damisa da kuraye.

  7. Jami'ar jihar Sokoto ta shirya gagarumin taro kan waƙoƙin Abubakar Kassu Zurmi

    Amsoshi

    Asalin hoton, Amsoshi

    Jami'ar Jihar Sokoto ta shirya gagarumin taron duniya kan tarihi da rayuwar fitaccen mawaƙin ƙasar Hausa da ya yi shura gomman shekaru da suka gabata, Abubakar Kassu Zurmi.

    Taron ya haɗa gogaggun masana al'adu da adabi da kimiyyar harshen Hausa daga ciki da wajen Najeriya, waɗanda suka yi jawabai tare da gabatar da muƙalu da suka shafi tarihin rayuwar mawaƙin, wanda ya rasu shekaru da suka gabata.

    Kazalika, an karrama wasu mawaƙan baka da sha'irai bisa waƙoƙin da suka wallafa masu nasaba da samar da haɗin kai da tsaro a Najeriya da makwabtan ƙasashe..

    ..

    Asalin hoton, Amsoshi

    Haka kuma wasu daga cikin fitattun waɗanda suka halarci taron sun bayar da gudunmowar kudi ga iyalan marigayi Abubakar Kasu Zurmi tare da wasu fitattun mawaƙan baka.

    Makada Abubakar Kassu Zurmi dai mawakin maza ne, da ya fi mayar da hankali a waƙoƙin noma da farauta da na ɓarayi da kuma 'yan tauri.

    Mutane

    Asalin hoton, Amsoshi

    Yakan yi amfani da salon kambamawa musamman ta zulake wani sa'in yabo a cikin waƙoƙinsa domin ya zuga gwarzayensa.

    Daga cikin waƙoƙinsa da suka yi fice akwai Shayi Dan Gidan Labbo da Dammande ada kuma Nomau Na Magarya

  8. Ƙungiyar JNIM ta ɗauki alhakin hari kan sojojin Benin

    mayaƙa

    Asalin hoton, others

    Rahotonni daga benin na cewa wata ƙungiya mai alaƙa da al Qaeda (JNIM) ta ɗauki alhakin kai mummunan hari kan wasu ofisoshin soji biyu a ƙasar.

    Wata majiyar sojojin ƙasar ta ce dakaru tawas ne suka mutu a lokacin harin na ranar Alhamis.

    To amma wata ƙungiyar Amurka da ke sa 'ido kan ayyukan masu iƙirarin jihadi, ta ce ƙungiyar JNIM ta yi iƙirarin kashe sojojin ƙasar 70 a lokacin harin.

    A baya-bayan ana ta samun ƙaruwar hare-haren masu iƙirarin jihadi a arewacin Benin.

    Benin ta yi iyaka da Burkina Faso da Nijar, waɗanda suka kwashe shekaru suna fama da hare-haren masu iƙirarjin jihadi.

  9. Qatar ta nuna damuwa kan daƙile yunƙurin tsagaita wuta a yaƙin Gaza

    QATAR

    Babban mai shiga tsakani na Qatar ya bayyana damuwarsa kan daƙile yunƙurin tsagaita wuta a yaƙin Gaza.

    Mohammed Al-Khulaifi ya faɗa wa kamfanin dillancin labaran Faransa cewa rayukan ɗimbin jama'a na cikin hatsari.

    Ya ce yunƙurin tattaunawa na ci gaba da jan ƙafa, inda ya yi gargaɗin cewa taɓarɓarewar yanayin jin ƙai idan yaƙin ya ci gaba.

    A ranar Asabar ne Hamas ta yi watsi da buƙatar tsagaita wuta ta kwana 45 da Isra'ila ta gabatar mata.

    Sarkin Qatar ya zargi Isra'ila da kasa mutunta sharuɗan yarjejeniyar da ta gabata.

    A watan da ya gabata ne Isra'ila ta koma ƙaddamar da hare-hare a Gaza, sakamakon zargin Hamas da ƙin amincewa da tsawaita kashin farko na yarjejeniyar tsagaita wutar.

  10. Najeriya ta mayar da ƴan Mali 62 da suka shiga ƙasar ba bisa ƙa'ida ba

    Kemi Nandap

    Asalin hoton, Kemi Nandap

    Hukumar shige da fice ta Najeriya ta tabbatar da mayar da wasu ƴan Mali 62 da suka shiga ƙasar ba bisa ƙa'ida ba.

    Cikin wata sanarwar da babban kwanturolan hukumar mai lura da kan iyakar Illela - inda ta nan ne aka fitar da mutanen - Tony Akuneme ce mutanan sun haɗa da maza 51 da kuma mata 11, kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar, NAN ya ruwaito.

    Mista Akuneme ya ce jami'an hukumar ne suka yi wa mutanen rakiya daga shalkwatar hukumar shige da fice ta ƙasa da ke Abuja zuwa kan iyakar Illela da ke jihar Sokoto, cikin motocin bas biyu.

    Ya ƙara da cewa bayan tanatance takardunsu, an miƙa su ga jami'an ƴansandan Nijar da ke Birnin Konni.

    A baya-bayan nan Najeriya mayar da ƴan ciranin da ke shiga ƙasar daga maƙwabtan ƙasashe ba tare da cikakkun takardun izini ba.

    A watannin da suka gabata ma ƙasar ta mayar da wasu gomman ƴan ƙasashen Mali da Togo da suka shiga ƙasar ba bisa ƙa'ida ba.

  11. Koriya ta Kudu ta dakatar da atisayen soji bayan kuskuren hari a yankin fararen hula

    Jirgin Yaƙi

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin saman Koriya ta Kudu ta ce ta dakatar da mafi yawan jiragen samanta, bayan da wasu jiragen yaƙi suka yi kuskuren jefa makamai kan wasu tankokin mai a lokacin wani atisaye a farkon makon nan.

    An jefa makaman ne a wani wuri da fararen hula ke harkokinsu, mai nisa kilomita 100 daga gabashin Seoul, babban birnin ƙasar.

    Ba a dai samu labari rasa rai ko jikkata a lokacin harin ba.

    Tuni ƙasar ta dakatar da babban atisayen haɗin gwiwa da take yi da Amurka.

    Atisayen da aka yi wa laƙabi da ''Tutar Ƴanci'' ana yinsa ne sau biyu a shekara, tare da jiragen sama fiye da 90.

    A watan da ya gabata wasu jiragen ƙasar biyu sun yi kuskuren jefa boma-bomai a wani yankin fararen hula, lamarin da ya yi sanadiyyar jikkata fiye da mutum 50.

  12. Netanyahu ya ce gwamnatinsa ba ta da zaɓi illa ci gaba da yaƙin Gaza

    Firaiministan Isra'ila ya ce gwamnatinsa ba ta da zaɓi illa ta ci gaba da yaƙin da take yi a Gaza.

    A kalamansa na farko tun bayan da ƙungiyar Hamas ta yi fatali da shawarar tsagaita wuta da Isra'ila ta gabatar, Benjamin Netanyahu ya ce rikicin ya kai wani muhimmin mataki.

    Mista Netanyahu ya ƙara da cewa ''muna wani mataki mai muhimmanci a yaƙin kuma a wannan lokacin ana buƙatar haƙuri da jajircewa domin yin nasara.''

    A jawabin da ya yi ta bidiyo, Netanyahu ya ce yaƙin Gaza ba zai ƙare ba har sai an murƙushe Hamas tare da maido da dukkan Isra'ilawan da ƙungiyar ke riƙe da su.

    Masu zanga-zangar neman a gaggauta dakatar da yaƙin sun yi arangama da ƴansanda a Mazor da ke tsakiyar Isra'ila inda Mista Netanyahu zai kai ziyara.

  13. 'Adadin waɗanda suka mutu a harin Benue ya kai 56'

    Hyacinth Iormem Alia

    Asalin hoton, Hyacinth Iormem Alia/Facebook

    Bayanan hoto, Gwamnan jihar Benue Hyacinth Iormem Alia

    Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia ya ce adadin waɗanda suka mutu a harin da wasu ƴanbindiga suka kai ƙananan hukumomin Ukum da Logo a jihar ya kai 56.

    Yayin da yake jawabi ga manema labarai bayan ya ziyarci garuruwan, Mista Alia ya bayyana harin da na jahilci da rashin imani.

    ''A yanzu da nake jawabi, mutum 56 ne suka mutu waɗanda ba su ji ba su gani ba, da suka haɗa da iyaye da maza da mata da ƙananan yara'', in ji shi.

    Gwamnan ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta gaggauta ɗaukar matakai domin kawo ƙarshen hare-hare a jihar.

    ''Al'ummarmu na da haƙƙin rayuwa cikin kwanciyar hankali, su yi noma su taso cikin iyalansu su reni ƴaƴansu ba tare da wata fargaba ba'', kamar yadda ya bayyana.

    Gwamnan ya ce ya gana da shugabannin al'umma da mutanen da harin ya shafa, inda ya saurari kokensu, tare da tabbatar musu cewa gwamnatin jihar na tare da su, ba za ta taɓa yin watsi da su ba.

    Mista Alia ya ce tuni gwamnatin jihar ta ƙara tura jami'an tsaro zuwa yankunan domin kwantar da hankula.

    Harin na zuwa ne kimanin mako biyu bayan wasu ƴanbindiga sun kashe fiye da mutum 100 a wasu hare-hare a jihar Plateau mai makwabtaka.

  14. Babu tabbas ko Fafaroma zai halarci bikin Easter Sunday a Fadarsa

    Paparoma

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, A baya-bayan nan Fafaroma Francis ya shafe fiye da wata guda a kance a asibiti

    Yayin da mabiya addinin kirista ke bukukuwan ''Easter Sunday'' wato Lahadi mai kyau a yau, akwai rashin tabbas kan ko Paparoma Francis zai halarci ɗaya daga cikin muhimman tarukan Easter da ake yi a Fadar Vatican.

    Wasu jami'an fadar sun ce Fafaroman zai halarci taron - wanda ake gudanarwa a fadar tasa.

    An dai saba a taron Fafaroma kan tsayawa a farfajiyar dandalin St Peter inda yake saka wa mutane albarka.

    Har yanzu akwai alamun rashin lafiya a tare da Fafaroma Francis mai shekara 88 a duniya bayan jinyar cutar sanyin haƙarƙari ta Pneumonia da ta kamashi, inda ya shafe fiye da wata guda a asibiti.

    Fafamaroman bai jagoranci wasu tarukan bikin Easter ba amma an ga ya bayyana bagatatan a wasu lokuta.

  15. Marabanku

    Masu bibiyarmu a wannan shafi na kai-tsaye kamar kullum, barkanmu da hutun ƙarshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku irin wainar da ake toyawa a sassan duniya daban-daban.

    Kada ku manta da damar da kuke da ita, ta bayyana ra'ayoyinku kan abubuwan da muke wallafa a shafukanmu na sada zumunta.