window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar 30/04/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Umar Mikail

  1. Tinubu ba ya katsalandan a ayyukan EFCC - Olukoyede

    Shugaban EFCC, Ola Olukoyede

    Asalin hoton, EFCC/Facebook

    Bayanan hoto, Shugaban EFCC, Ola Olukoyede

    Shugaban hukumar EFCC, mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya, Ola Olukoyede, ya yi watsi da zarge-zargen da ake yi wa Shugaban Ƙasar Bola Tinubu, na yin amfani da hukumar wajen muzguna wa jam'iyyun adawa.

    Yayin wata zantawa da gidan talbijin na Channels ta cikin shirin 'Politics Today' a ranar Laraba, Mista Olukoyede ya bayyana zarge-zargen da yunƙurin kawar da hankalin shugaban ƙasar daga ''kyawawan ayyukan da yake yi.''

    Shugaban EFCCn ya ce babban abin da ke gaban shugaban ƙasar bai wuce yadda manyan ma'aikatu da hukumomin gwamnati ke gudanar da ayyukansu ba.

    “Shugaban ƙasa ba shi da lokacin ɓatawa, mutane ne kawai ke son kawar da hankalinsa. Amma waɗanda ke kusa da shi za su faɗa maka cewa babu abin da yake son ji illa ƙoƙarin ingantuwar gwamnati'', in ji Mista Olukoyede.

    A Najeriya dai an jima ana zargin hukumomi irin EFCC da zama karen farautar gwamnatocin da ke kan mulki da jam'iyyunsu wajen muzguna wa ƴan hamayya.

    To sai dai Mista Olukoyede ya kare zarge-zargen da cewa hukumar EFCC ta kama mambobin jam'iyyar APC mai mulki masu yawa da suka aikata ba daidai ba fiye da na jam'iyyun hamayya.

  2. Amurka ta saki wani ɗalibi Bafalasɗine da aka tsare a ƙasar

    Hukumomin Amurka sun yi biyayya ga umarnin kotu inda suka saki ɗalibi ɗan Falasɗinu da jami'an shige da fice suka tsare a farkon watan nan.

    Mohsen Mahdawi ɗaya ne daga cikin ɗalibai masu fafutukar nuna goyon baya ga Falasɗinawa da gwamnatin Trump ta yi ƙoƙarin tisa ƙeyarsu ƙarƙashin wata doka da tun asali aka yi amfani da ita wajen korar ƴan gurguzu.

    Lauyoyin ɗalibin na jami'ar Columbia sun zargi gwamnati da tsare shi a matsayin ramuwar gayya kan fafutukar da ya yi.

    Sun bayyana iƙirarin hukumomi kan ɗalibin a matsayin mara tushe bare makama kuma abin kunya ga kundin tsarin mulkin Amurka.

  3. Gwamnatin Najeriya ta ayyana gobe Alhamis a matsayin ranar hutu a ƙasar

    Shugaba Tinubu

    Asalin hoton, Tinubu/X

    Gwamnatin Najeriya ta ayyana gobe Alhamis 1 ga watan Mayu a matsayin ranar hutu ga ma'aikatan a ƙasar don bikin murnar ranar ma'aikata ta duniya.

    Ana gudanar da bikin ranar ma'aikata a ranar 1 ga watan Mayun kowace shekara.

    Cikin wata sanarwa da ministan harkokin cikin gida na ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo, ya fitar ya yaba wa ma'aikatan ƙasar kan sadaukarwa da jajircewar da suke yi wajen gudanar da ayyukansu.

    Ministan ya kuma yaba musu kan gudunmowar da suke bayarwa wajen ciyar da Najeriya gaba

  4. Tattalin arzikin Amurka ya ragu karon farko cikin shekara uku

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Tattalin arzikin Amurka ya ragu a karon farko cikin shekara uku. Matakin na zuwa ne watannin bayan komawar Donald Trump mulkin ƙasar.

    Yawan arzikin da asar ke samu a cikin gida ya ragu da kashi 0.3 a cikin wata ukun farkon shekarar nan.

    Masu sharhi sun alaƙanta raguwar da tsare-tsaren gwamnatin Trump kan tattalin arziki, saboda yadda masu sarin kaya suna daina shigar da kaya sakamakon ƙaruwar haraji.

    Alƙaluman sun ƙara haifar da fargabar faɗawar ƙasar komar tattalin arziki.

    Sai dai Shugaba Turmp ya ɗora alhakin hakan kan tsohon shugaban ƙasar Jor Biden.

    Yayin da yake jawabi a taron ministocinsa, Mista Trump ya jaddada da cewa faɗuwar tattalin arzikin ba shi da alaƙa da ƙarin harajin da ya yi.

  5. Isra'ila ta ce ta kai farmaki kan ''masu tsattsauran ra'ayi'' a Syria

    Firaiministan Isra'ila da ministan tsaronsa sun ce sojojin ƙasar sun kai farmaki kan abin da suka kira masu tsattsauran ra'ayi a Syria da ke shirin kai hari kan ƴan ƙabilar Druze marasa rinjaye a kusa da Damascus.

    Cikin wata sanarwar haɗin gwiwa, sun ce Isra'ila ta aika wani saƙo ga mahukuntan Syria don su kare al'ummar Druze.

    Tun da farko kafafen yaɗa labaran Syria sun ruwaito cewa aƙalla sojoji goma 11 ne aka kashe lokacin da aka kai hari kan sansanin sojinsu a garin Druze.

    Ma'aikatar harkokin cikin gida ta sha alwashin murƙushe duk wanda aka samu yana ƙoƙarin tayar da zaune tsaye a ƙasar.

    Harin na jiya Talata ya zo ne sakamakon rikicin ƙabilanci da ya faru tsakanin wasu ƴan ƙabilar Druze da wasu daga yankunan ƴan Sunni, lamarin da ya janyo mutuwar aƙalla mutum tara.

  6. Jagororin Indiya sun gudanar da taro yayin da zaman tankiya tsakaninta da Pakistan ke ƙara ta'azzara

    Modi

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaiministan Indiya Narendra Modi, ya gudanar da wasu manyan taruka da ƴan majalisar zartarwarsa da manyan ƴan siyasa da masu faɗa-a-ji da kuma manyan jami'an tsaro daidai lokacin da ake ƙara samun zaman ɗar-ɗar tsakanin ƙasarsa da maƙwabciyarta Pakistan.

    Zuwa yanzu babu wani martani da aka ji daga gwamnatin ƙasar ta India ko kuma abubuwan da aka cimma a tarukan da firaiminsitan ya gudanar.

    Gwamnatin Mista Modi na fuskantar matsin lamba kan ta mayar da martani bayan da ta sha zargin hukumomin Pakistan da goyon bayan ƴan awaren Kashmiri da suka ƙaddamar da mummunan hari kan masu yawon buɗe ido a makon da ya gabata.

    Mutum 26 aka kashe, wasu da dama kuma suka ji rauni.

    Tun da farko a jiya Talata, ministan yaɗa labaran Pakistan ya ce gwamnatinsa ta samu wasu bayanan sirri na yiwuwar hari daga Indiya, sai dai bai yi wani ƙarin haske ba.

    Ya ce Pakistan na ƙara nanata cewa idan sojojin Indiya suka kuskura suka yi ganganci a ƙasarsa, za su ɗauki mataki.

    Pakistan na ƙara nanata ƙudirinta na kare yancinta a kowane yanayi.

  7. Shaguna kusan 500 ne suka ƙone a kasuwar Terminus ta Jos

    Kasuwar Terminus

    Asalin hoton, Nema

    Shaguna kusan 500 ne suka ƙone ƙurmus sanadin tashin gobara a babbar kasuwar Jos da aka fi sani da Terminus a jihar Filato ta tsakiyar Najeriya.

    Yankasuwar sun ce gobarar ta tashi ne da tsakar daren jiya Talata kuma sun yi asarar dukiya ta miliyoyin naira.

    Hukumar agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta ce mutum 309 ne shuganansu suka ƙone tare da kayan ciki, sai wasu 58 da 'yandaba suka wawashe.

    Mustapha Ibrahim Bako, shi ne shugaban kasuwar ta Terminus kuma ya faɗa wa BBC cewa rashin zuwan motocin kashe gobara da wuri ne ya jawo ta'azzarar ɓarnar.

    "Halin da ake ciki babu daɗi, a jiya mun kwashe mutane sun fi 10 saboda hayaƙin da suka shaƙa, wasu kuma firgici," in ji shi.

    Ya nemi gwamnatin jihar da "kada ta ce za ta kori kowa a kasuwar, saboda akwai wuraren da wutar ba ta shafa ba, a ƙyale su su ci gaba da kasuwancinsu".

  8. Majalisar Shari'ar Musulunci ta Najeriya ta naɗa Sheikh Bashir shugabanta

    Sheikh Bashir Aliyu Umar

    Asalin hoton, Facebook/Bashir Aliyu Umar

    Majalisar Shari'ar Musulunci ta Najeriya ta naɗa Sheikh Bashir Aliyu Umar a matsayin shugabanta bayan rasuwar Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.

    Wata sanarwa da majalisar ta fitar a yau Laraba ta ce an amince da shuagabancin Dr Bashir ne kai-tsaye saboda kasancewarsa mataimakin shugaba.

    A ranar Litinin ne Sheikh Hadiyyatullah ya rasu yana da shekara 81 a jihar Osun da ke kudancin Najeriya.

    "Nan gaba za a sanar da mataimakin shugaban," in ji sanarwar da Nafiu Baba Ahmed ya sanya wa hannu a matsayin sakataren majalisar.

    Sheikh Bashir sanannen malami ne kuma shi ne babban limamin masallacin Juma'a na Al-Furqan da ke jihar Kano.

  9. Pakistan ta ce Indiya na shirin kai mata hare-haren soji yau ko gobe

    Sojojin Indiya

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan yaɗa labarai na Pakistan ya ce ƙasarsa na da "bayanan sirri" cewa Indiya na shirin kai musu hari cikin awa 24 ko 36 masu zuwa.

    Kalaman na Attaullah Tarar na zuwa ne bayan Indiya ta zargi Pakistan da taimaka wa 'yanbindigar da suka kashe masu yawon buɗe-ido 28 a yankin Kashmir na ɓangaren Indiyar.

    Tarar ya ce Indiya na shirin amfani da harin a matsayin dalili na kai wa Pakistan hari, yana cewa "tabbas za su mayar da martani kan duk wani hari daga Indiya".

    BBC ta nemi jin ta bakin ma'aikatar harkokin wajen Indiya, amma zuwa lokacin haɗa wannan rahoton ba ta ce komai ba.

    Harin da aka kai a kusa da garin Pahalgam shi ne mafi muni a kan fararen hula cikin shekara 20 a yankin da ƙasashen ke taƙaddama a kai.

    Indiya da Pakistan sun gwabza yaƙi sau biyu a kan yankin Kashmir, inda daga baya aka raba shi a tsakaninsu.

  10. Daga ina 'mutane masu shan jini' suka samo asali?

    Vampires

    Asalin hoton, Getty Images

    A farkon ƙarni na 18, gomman mutane a Serbia sun riƙa yin wata mutuwa mai cike da ban mamaki, inda aka yi zargin cewa maƙwafcinsu da ya mutu ne ke bibiyar su, sai su ji kamar an shaƙe su ko kuma suna numfashi cikin wahala kafin su mutu.

    Musamman wasu ƙananan kauyuka biyu, Medvedja da ke kudancin ƙasar Serbia da kuma Kisiljevo a arewa maso yammaci, nan ne aka fi samun raɗe-raɗin mutuwar.

    Ƙauyukan na da nisan kilomita 200 tsakaninsu, amma sun bayar da rahotannin abubuwan ban mamaki masu kama da juna cikin shekara 10.

    An aiko likitoci daga ƙasar Austria domin su binciki dalilan da suka yi sanadin mutuwar, kuma sun tattara cikakken rahoton abubuwan da suka gano. Cikin gaggawa rahoton bincikensu ya isa ga kafafen yaɗa labaran Austria daga baya kuma zuwa ga masu bincike a makarantu.

    Masanin tarihi na Jamus, Thomas M Bohn, wanda ya wallafa littafin 'Vampires: The Origin of the European Myth', ya ce daga haka ne aka samo kalmar 'Vampire', a wata jarida mai suna ‘Wienerisches Diarium’ a shekarar 1725.

  11. Zaɓen Okowa a matsayin abokin takara ne ya kayar da Atiku a 2023 - Abba Moro

    Sanata Abba Moro

    Asalin hoton, Channels TV

    Shugaban marasa rinjaye a Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Abba Moro, ya yi ikirarin cewa zaɓar Ifeanyi Okowa a matsayin abokin takarar shugaban ƙasa ne ya sa Atiku Abubakar ya yi rashin nasara a zaɓen 2023.

    Sanata Moro na mayar da martani ne game da kalaman Okowa cewa ya yi nadamar yin takara tare da Atiku a jam'iyyar adawa ta PDP.

    Okowa ya yi kalaman ne bayan ya bar PDP tare da komawa jam'iyyar APC mai mulkn Najeriyai a ranar Litinin.

    Sai dai Moro ya siffanta kalaman na Okowa da "rashin godiya", yana mai cewa tsohon gwamnan na Delta ne da kansa ya nemi takarar "saboda haka bai kamata ya nesanta kansa daga abin da ya faru ba".

    "Wasu na cewa akwai mutanen da suka hidimta wa jam'iyyar f[iye da Okowa] kuma za su fi taimaka mata wajen cin zaɓen sama da shi," in ji Moro a hira da Channels TV.

    "Ina ganin zaɓen Okowa a matsayin abokin takarar shugaban ƙasa a 2023 babban kuskure ne."

  12. Binciken BBC ya gano sansanonin sojin Turkiyya 136 a Iraƙi

    Iraƙi

    Asalin hoton, Phil Caller

    Wani bincike da BBC ta gudanar ya nuna girman ƙaruwar sojojin Turkiyya a arewacin Iraki, inda Ankara ke cewa tana rarakar mayakan Kurdawa na PKK.

    Wakiliyar BBC ta ce an gano sansanonin sojin Turkiyya har 136 ta hanyar amfani da hotunan tauraron ɗan'adam, inda aka gina 121 a filayen noma masu albarka tun daga shekarar 2018.

    Binciken ya gano cewa gwamnatin jeka-na-yi-ka ta Kurdawa a yankin ba ta nuna damuwa kan hakan, kuma mutane ƙalilan ne ke korafin take hakkinsu, saboda matakin na Turkiyya.

    Gwamnatin Turkiyya ta ƙi mayar da martani game da batun.

  13. Gwamnatin Nijar ta ɗauke wa sababbin kamfanoni biyar haraji

    Lamin Zaine

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Firaministan Nijar Lamine Zaine

    Gwamnatin mulkin sojan Nijar ta bayar da lasisin kafa wasu kamfanoni biyar da ta ɗauke wa haraji na wani lokaci domin ƙarfafa musu gwiwa.

    Kamfanonin sun haɗa da na sarrafa ƙarafuna da wayoyin gine-gine, da wanda zai samar da makamashin lantarki da sayar da manyan injinan wutar.

    Akwai kuma mai sarrafa sabulai da sauran kayan tsafta, da wanda zai sarrafa kayan gona, da mai samar da magunguna a kasar.

    Wakiliyar BBC a Nijar Tchima Ila ta ce waɗannan kamfanoni biyar za su samar da guraben aiki na dindindin kusan 3,000, da wasu dubbai na wucin gadi a shekaru biyar masu zuwa, musamman ga matasa.

    Kamfanonin za su saka jarin da ya kai kusan cfa biliyan 250 a shekarun farko na soma aikin nasu.

  14. 'Yansandan Sweden sun kama matashin da ya harbe mutum uku

    'Yansanda a Sweden

    Asalin hoton, EPA

    Rundunar 'yansandan Sweden ta kama matashin da ya harbe mutum uku a birnin Uppsala ranar Talata.

    An ce maharbin ya tsere ne a kan keken scooter bayan harbe-harben a wani shagon gyaran gashi.

    'Yansanda sun tabbatar a yau Laraba cewa matashin da suka kama bai kai shekara 18 ba.

    Mutanen uku da ya kashe shekarunsu 15 ne zuwa 20, kamar yadda 'yansanda suka bayyana a taron manema labarai.

  15. Ɗanbindiga ya harbe mutum uku a Sweden

    Kisan gilla a Sweden

    Asalin hoton, EPA

    Mutum uku sun mutu sakamakon harbin bindiga a birnin Uppsala na Swededn, a cewar rundunar 'yansandan ƙasar.

    Harbin ya faru ne a wani shagon gyaran gashi da ke tsakiyar birnin, in ji rahoton wata kafar yaɗa labarai a ƙasar.

    Sai dai har yanzu ba a kama wanda ya yi kisan ba, wanda ya tsere a kan keken scooter.

    Jami'an tsaro su rufe hanyar zuwa wurin kuma sun fara binciken lamarin a matsayin kisan gilla.

    Lamarin ya faru ne a jajiberin bikin Walpurgis, inda dubban mutane ke taruwa a Uppsala da ke arewacin ƙasar.

  16. 'Yan Najeriya 203 da suka maƙale a Libya sun koma gida

    'Yan Najeriya daga Libya

    Asalin hoton, Nema

    Hukumar agajin gaggawa a Najeriya ta ce ta karɓi 'yan ƙasar 203 da aka kwaso daga Libya bayan sun kasa fitowa daga ƙasar ta arewacin Afirka.

    Jim kaɗan bayan isarsu filin jirgin sama na Murtala Muhammed a Legas a jiya Litinin ne jami'an hukumar ta tarɓe su.

    Jirgin kamfanin Al Buraq ne ya kwaso mutanen, waɗanda suka ƙunshi maza manya 50, mata manya 96, da yara 29, da kuma jarirai 28.

    Ƙungiyar kula da ƙaura ta duniya wato International Organisation for Migration (IOM) ce ta ɗauki nauyin mayar da su gida bisa haɗin gwiwa da hukumar National Emergency Management Agency (Nema) da sauran hukumomi.

    Wata sanarwa da Nema ta fitar ranar Talata ta ce biyu daga cikin mutanen na buƙatar kulawar gaggawa, "kuma nan take aka kai su asibitin Ikeja domin duba su".

  17. Shugaban Koriya ta Arewa ya ba da umarnin shirya makamin nukiliya

    Shugaba Kim Jong Un

    Asalin hoton, Reuters

    Kafofin yaɗa labara a Koriya ta Arewa sun ce Shugaba Kim Jong-un ya umarci rundunar sojin ruwansa da ta gaggauta kai makaman nukiliya jiragen ruwa.

    Kamfanin dillancin labaran a Koriya ta Kudu sun ce an bayar da umarnin ne bayan shugaban Koriya ta Arewa ya sa ido kan gwajin makaman da ƙasarsa ta yi na baya-bayan nan.

    Masana sun ce akwai yiyuwar a ɗaura wa jiragen ƙananan makaman nukiliya masu cin gajeren zango.

    Mista Kim ya kuma ƙaddamar da ƙarin wani katafaren jirgin ruwa da za a iya amfani da shi wajen harba makamin na nukiliya.

  18. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake haɗuwa a shafin labarai kai-tsaye na yau Laraba.

    Za mu fi mayar da hankali kan Najeriya da Nijar da maƙwabtansu.

    Umar Mikail ne ke muku maraba a wannan hantsi.