Yadda ƙananan yara ke fama da matsanancin ƙarancin abinci a Katsina

Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
Yadda ƙananan yara ke fama da matsanancin ƙarancin abinci a Katsina

Mummunar matsalar ƙarancin abinci mai gina jiki ta yi ƙamari a jihohi shida na Arewacin Najeriya, wani lamari mai matuƙar tayar da hankali, inda matsalar ta shafi yara ‘yan ƙasa da shekara biyar miliyan 4.4 da mata masu juna biyu kusan 600,000, a cewar Shirin Samar da Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP).

Matsalar na ci gaba da yaɗuwa cikin sauri: Shirin Samar da Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya ya ce adadin yaran da ke fama da matsalar ya ninka fiye da sau biyu idan aka kwatanta da bara.