Ku San Malamanku tare da Sheikh Yusuf Sambo Rigachikun

Bayanan bidiyo,
Ku San Malamanku tare da Sheikh Yusuf Sambo Rigachikun

Sheikh Yusuf Muhammad Sambo Rigachikun, yana ɗaya daga cikin fitattun malaman addinin Musulunci a Najeriya, mazaunin jihar Kaduna, amma a wannan zantawa ya ce ya taso ne a garin Funtua, a can ya fara dasa ɗan ba na karatunsa.

An haifi fitaccen malamin a garin Tsibiri cikin ƙaramar hukumar Giwa.

Sheikh Sambo Rigachikun a cikin shirin Ku San Malamanku na wannan mako, ya ce ya koma Zariya ne sanadin gidan jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo.

Daga cikin manyan malaman da ya yi karatu a wajen su akwai Mallam Chado Funtua da Mallam Alu na Rimin Tsiwa da Mallam Adamu da ke Unguwar Ƙofar Doka da marigayi Sheikh Abubakar Muhmud Gumi.

Muslim Cleric