window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni dangane da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya 15/05/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Nabeela Mukhtar Uba da Aisha Babangida

  1. Najeriya za ta ƙaddamar da taurarin ɗan'adam saboda tsaro

    Gwamnatin Najeria ta bayyana cewa za ta ƙaddamar da tauraron ɗan'adam guda huɗu da za su taimaka wajen lura da yanayin ƙasa da kuma yaƙi da matsalolin tsaro da ake fama da su.

    Wadannan taurarin dan'adam ɗin za a yi amfani da su wajen nazarin dazuka da kai kawon jama’a da kuma wadda za ta ɗauko hotunan tekuna da tsaunuka da kuma gano sauran ma’adinai.

    Ministan sadarwa da fasahar zamani na ƙasar Uche Nnaji ne ya bayyana hakan a lokacin wani taron majalisar zartaswa ta ƙasa da ya shafi kirkira da fasahohin zamani karo na ashirin da biyu, wanda ya gudana a babban birnin ƙasar Abuja.

    Gwamnatin dai ta ce za ta ƙaddamar da waɗannan taurarin ɗan'adam ne domin gudanar da muhimman ayyukan da suka shafi saka ido a kan yankuna da wuraren da ke fama da matsalar tsaro da kuma ɗaukar muhimman hotunan ƙasa da suka shafi tsaunuka da ruwan ƙasar da ma sauran su

  2. Sudan ta Kudu ta musanta mutuwar shugabanta

    Salva Kirr

    Asalin hoton, AFP

    Gwamnatin Sudan ta Kudu ta musanta rahotannin da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta cewa shugaba Salva Kirr Mayardit ya rasu.

    Gwamnatin ta ce rahotannin ƙarya ce marar makama.

    Ma'aikatar harkokin wajen ƙasar ta ce shugaba Salva Kirr yana nan da rai, kuma labaran wata hanya ce ta kawo ruɗani.

    A baya bayan nan shugaban ya naɗa makusancinsa a matsayin mataimaki, lamarin da ya janyo raɗe-raɗin cewa matakin wani yunƙuri ne na samun wanda zai gaji shugaban ƙasan saboda taɓarɓarewar lafiyar sa.

    Gwamnatin dai ta sha musanta rahotannin rashin lafiyar shugaba Salva Kirr.

  3. Amurka ta damu da halin da ake ciki a Gaza - Rubio

    Rubio

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, ya ce gwamnatin Trump ta damu matuƙa da halin da ake ciki a Gaza musamman ta fuskar agaji wanda toshe duk wasu hanyoyin shigar da kayan agaji da Isra'ila ta yi ya haddasa.

    Ya ce Amurka ta damu da irin uƙubar da al'ummar Gaza ke sha, to amma duk da haka ya nanata matsayin Amurkan a kan cewa dole a ɗora alhakin hakan a kan 'yan ƙungiyar Hamas.

    Mr Rubio, ya yi wannan jawabin ne a yayin da aka kashe Falasɗinawa fiye da 100 a wasu sabbin hare-hare ta sama da Isra'ila ta kai.

    Yawancin waɗanda suka mutu mata da yara ne da ke zaune a sansanonin 'yan gudun hijirah.

    Isra'ila ta ce ta kai hare-haren a kan "'yan ta'adda".

  4. An yanke wa ƴan China huɗu hukuncin zaman gidan kaso na shekara 20 a Plateau

    A Najeriya, wata babbar kotun tarayya da ke zama a jos, babban birnin jihar Filato, ta kama wasu 'yan kasar Sin huɗu da laifin hada-hadar da ta shafi harkar haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba, kuma ta yanke masu hukunci ɗaurin shekara 20 a gidan maza.

    Mutanen hudu 'yan kasar Sin (wato China) da babbar kotun tarayya da ke Jos ta kama da laifin, sun hada da Yian Quin Yong (Liang Quin Yong), da Wan Hwajii (Wang Huajie), da Zyon Jiyajin (Zhong Jiajing) da kuma Long Kechong (Long Kechong). Wadanda ta yanke wa hukuncin daurin shekara biyar-biyar a jarun kowannensu, ko kuma zabin biyan tarar kudi naira miliyan dai-dai.

    Sakamakon samun su da laifin sayen ma'adinai ba bisa doka ba, a ranar tara ga watan Maris da ya gabata a yankin birnin Jos na jihar Filato.

    Babbar kotun tarayyar ta kuma bayar da umarnin a fitar da su daga Najeriya, tare da haramta masu sake shigowa kasar haihata-haita.

    Bugu da kari, kotun ta bayar da umarnin karbe daukacin ma'adinan da aka gano a lokacin gudanar da bincike, da kuma tsabar kudi naira miliyan goma sha shida da dubu dari uku, a matsayin wata tara, saboda kin bayyana harkar kudi cikin kwanaki bakwai ga sashe na musamman da ke aikin dakile hada-hadar halatta kudin haram a Najeriya.

    Hukunce-hukunce dai sun biyo bayan amsa laifukan da wadanda aka tuhuma suka yi ne, kuma kotun ta gamsu da bayana da aka gabatar mata a kan tuhume-tuhumen da aka yi masu.

  5. 'Dakatar da tallafin USAID ba zai hana mu yaƙi da cutar HIV ba'

    Ministan lafiyan ƙasar Afirka ta Kudu, ya ce dakatar da tallafin da Amurka ta yi a kan shirin yaƙi da cuta mai karya garkuwar jiki ta HIV, ba zai hana ci gaba da shirin yaƙi da cutar ba a ƙasar.

    Amurka wadda ita ce ke bada kashi ɗaya cikin biyar na kuɗaɗen da ake amfani da su wajen yaƙi da cutar a Afirka ta Kudu ta dakatar bayan shugaba Trump ya hau kan mulki.

    An samu raguwa a mutanen da ke zuwa gwajin cutar tun bayan cire tallafin.

    Afirka ta Kudu na daga cikin ƙasashen da ke fama da masu cutar ta HIV a duniya inda take da mutum miliyan takwas.

  6. Sabbin shugabannin Syria na son ƙulla alaƙa da Israel

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce sabbin shugabannin Syria na son zaman lafiya da Isra'ila, sannan sun yi alƙawarin aiki ga al'ummar ƙasar da ta ƙunshi mutane da dama.

    Mr Rubio, na bayanin ne bayan tattaunawa a kan yadda za a daidaita dangantaka tare da takwaransa na Syria, Assad al Shaibani a Turkiyya.

    Sakataren harkokin wajen na Amurka ya ce ƙasarsa za ta yi duk mai yiwuwa wajen taimakawa a samu zaman lafiya da cigaba a Syria.

    A ranar Talata, shugaba Trump ya sanar da ɗage dukkan takunkuman da aka sanya wa Syria, har ma ya gana da sabon shugaban ƙasar, Ahmad al Sharaa a Riyadh.

  7. A shirye nake na tattauna da Putin - Zalennsky

    Zalensky

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky, ya ce har yanzu a shirye yake ya tattauna da shugaba Putin na Rasha, to amma Rasha ba ta ɗauki tattaunawar da muhimmanci ba.

    Yana wannan bayanin ne a Turkiyya, inda ya gana da shugaba Erdogan.

    Mr Zelensky, ya zargi Rasha da rashin martaba da Turkiyya da kuma Amurka bayan da Rasha ta aika da ƙaramar tawaga zuwa Istanbul domin tattaunawa, sakamakon ƙin halartar da Mr Putin ya yi.

    To amma ya ce shi tuni ya aike da tasa tawagar ƙarƙashin jagorancin ministan harkokin tsaron ƙasarsa.

  8. Duk wanda bai zaɓi mahaifina ba to za a kore shi daga Uganda - Janar Muhoozi

    Uganda

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban rundunar Sojin Uganda ya ce duk wanda yaƙi zaɓar mahaifinsa, shugaba Yoweri Museveni a babban zaɓen ƙasar da za a yi a watan Janairun shekara mai kamawa to za a kore shi daga ƙasar.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Janar Muhoozi Kainerugaba, wanda shi ne magajin Mr Museveni, bai bayyana inda za a mayar da mutanen da suka ƙi zaɓar mahaifin nasa ba.

    Kazalika janar ɗin ya wallafa wani saƙo a shafin nasa na X ranar Alhamis, inda ya ce sojoji mata yanzu za su rinƙa sanya siket, kuma duk wadda aka gan ta da dogon wando a to za ta ɗanɗana kudarta.

    A farkon watan nan na Mayu ne ya bayyana cewa ya kama tare da azabtar da wani mai tsaron babban ɗan adawar ƙasar, Bobi Wine.

  9. Amuka da Iran na gab da cimma matsaya kan shirin makamin nukiliya

    US/IRAN

    Asalin hoton, AP

    Shugaba Donald Trump ya ce Iran ta kama hanyar amincewa da ƙa'idojin mallakar makaman nukiliya da Amurka.

    Trump ya ce tattunawar ƙasashen biyu da aka kammala a ranar Lahadi za ta taimaka wajen samar da zaman lafiya.

    Tun da farko wani mai bai wa shugaban Iran shawara ya shaida wa NBC cewa Tehran a shirye take ta sassauta shirinta na nukiliya idan har za a ɗage takunkumin da aka ƙaƙaba mata.

    Amurka ta jajirce cewa dole Iran ta sassauta shirin nata na mallakar makaman nukiliya, amma Tehran ta ce tana shirin nata ne ba da nufin tayar da rikici ba.

    Da ya ke magana a ziyara da ya kai Qatar, shugaba Trump ya ce an kusa cimma yarjejeniya kuma hakan na nufin Amurka za ta kaucewa kai harin soji kan Iran.

    A ranar Lahadi aka kammala tattaunawa tsakanin ƙasashen biyu game da mallakar makaman nukiliyan, kuma dukkan su sun amince za su ci gaba da tattaunawa a kai nan gaba.

  10. DSS sun maka Pat Utomi a kotu kan kafa gwamnatin je-ka-na-yi-ka

    Farfesa Pat Utomi

    Asalin hoton, Pat Utomi/X

    A Najeriya Hukumar ‘yan sandan farinka DSS ta ya maka dan takarar shugaban kasar karkashin jam’iyyar African Democratic Congress, Farfesa Patrick Okedinachi Utomi, a kotu bisa zargin sa da kafa gwamnatin je-ka-na-yi-ka a kasar.

    Hukumar ta DSS dai ta shigar da ƙarar ne a babbar kotun tarayya da ke Abuja, inda ta ke ƙalubalantar wanda ake zargin da ƙoƙarin haddasa rikici da kuma yin barazana ga lamurran tsaron a Najeriya.

    Bayanin wanda kamfanin dillancin labaran Najeriyar, NAN, ya ruwaito, jam'ian na DSS sun shigar da ƙarar a ranar 13 ga wannan watan na Mayu ta hannun babban lauyan Najeriya, Akinlolu Kehinde inda suka bayyana matakin na farfesa Utomi a matsayin neman haddasa rikici a ƙasar.

    Farfesa Patrick Utomi ya taɓa tsayawa takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar African Democratic Congress a 2007.

    DSS dai ta ce tun da farko gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace wajen nusar da jagoran gwamnatin je-ka-na-yi-kan cewa abin da yake ƙoƙarin gudanarwa a ƙasar haramtacce ne, sai dai ya yi watsi da wannan tayin, inda ya yi gaban kansa.

  11. Hare-haren Isra'ila a Gaza sun kashe mutum 114

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Aƙalla Falasɗinawa 114 suka mutu sakamakon hare-haren sama da Isra'ila ta rinƙa kaiwa tun da asuba a zirin Gaza, kamar yadda jami'an lafiya da masu aikin ceto suka shaida.

    An kashe mutum 56 da suka haɗa da mata da yara a gidaje datanti-tantinsu inda suke gudun hijira bayan an jefa musu bama-bamai a kudancin birnin Khan Younis, in jiasibitin Nasser.

    Sojojin Isra'ila sun ce sun kai wa Hamas da ƙungiyar jihadi ta Falasɗinawa a kudancin Gaza.

    Rundunar tsaro ta Civil Defence ta ce munanan hare-hare a arewacin garin Jabalia da suka haɗa da hare-haren kan asibitoci da masallatai a sansanin ƴan gudun hijra na Jabalia abin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 13.

  12. Hauhawar farashi ta faɗo da kaso 23.71 a Najeriya - NBS

    NBS

    Asalin hoton, Getty Images

    An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga kashi 24.23 a watan Maris ɗin 2025 zuwa kashi 23.71 a watan Afrilun 2025.

    Hukumar Ƙididdiga ta Najeriya, NBS ta ce hauhawar farashin da aka samu a watan Afriliu ya nuna an samu ragin kaso 0.52 na hauhawar idan aka kwatanta da watan Maris.

    “Wannan na nuni da cewa hauhawar farashin Ta shekara-shekara Ta ragu a watan Afrilun 2025 idan aka kwatanta da watan Afrilun 2024."

    Dangane kuma da hauhawar farashin kayan abinci a watan Afrilun 2025 ta kasance kaso 21.26 kamar yadda ke faruwa a shekara-shekara.

  13. Ko ya halatta Trump ya karɓi kyautar jirgin alfarma daga Qatar?

    Trump

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce zai zama tamkar "sakarai" idan ya mayar da hannun kyauta baya dangane da kyautar jirgin da ƙasar Qatar ta ba shi mai ƙimar dala miliyan 400.

    To sai dai ƴan jam'iyyar hamayya sun bayyana karɓar kyautar da "abin da ya saɓa doka", wani abu da fadar White House ta musanta - kuma hakan ya janyo suka daga magoya bayan Donald Trump.

    Sashen BBC mai bincike ya yi nazari kan abin da doka ta ce ga shugabanni su karɓi kyautuka.

    A ranar Lahadi ne kafafen watsa labaran Amurka suka rawaito cewa gwamnatin Amurka na shirin karɓar babban jirgi sama ƙirar Boeing daga gidan sarautar Qatar - inda suke cewa za a sake ƙawata jirgin domin kasancewa jirgin shugaban ƙasar na Amurka.

  14. Indiya na son cire haraji kan kayayyakin Amurka - Trump

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙasar Amurka Donald Trump ya ce ƙasar Indiya ta ba da tayin cire dukkan haraji akan kayayyakin da ake shigo da su daga Amurka.

    Trump ya bayyana hakan ne a wani taro da wasu manyan ‘yan kasuwa da ya halarta a birnin Doha, inda ya ce: "Gwamnatin Indiya ta ba mu tayin yarjejeniya inda za su cire haraji gaba ɗaya."

    A halin yanzu, Indiya da Amurka na cikin tattaunawa kan kulla yarjejeniyar kasuwanci.

    Amma kuma har yanzu gwamnatin Indiya ba ta yi wani bayani ba dangane da wannan furuci na Trump.

    BBC ta tuntubi ma’aikatar kasuwanci ta Indiya don jin ta bakin su amma babu wasu cikakkun bayanai da aka fitar kan wannan tayin yarjejeniya da Trump ya ambata.

    Shugaban Amurkan ya kuma sanar da wasu sabbin yarjejeniyoyi tsakanin Amurka da Qatar, ciki har da siyan jiragen saman Boeing.

  15. Majalisa ta buƙaci a samar cibiyar rubuta JAMB a kowace ƙaramar hukuma

    ....

    Asalin hoton, Facebook/JAMB

    Majalisar Wakilan Najeriya ta buƙaci a samar da cibiyar rubuta Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu ta UTME guda ɗaya aƙalla a kowace ƙaramar hukuma cikin ƙananan hukumomi 774 da ke faɗin ƙasar.

    Ƴanmajalisar sun bayyana hakan ne a zaman majalisa da suka gudanar a ranar Alhamis, bayan da Hukumar JAMB ta amsa samun matsalolin da suka shafi gudanar da jarrabawar bana ta 2025.

    A cewar 'yan majalisar, samar da waɗannan cibiyoyin zai taimaka wajen hana maimaituwar irin waɗannan matsalolin a nan gaba.

    Majalisar ta kuma buƙaci ɗalibai da iyaye su kwantar da hankalinsu bayan amincewar JAMB cewa an samu kura-kurai a jarrabawar bana.

    A bara, Majalisar Dattawa ta kawo irin wannan ƙudiri, inda ta ce za a ware kudi a kasafin shekarar 2026 domin samar da cibiyoyin rubuta jarabawar jamb (CBT) a dukkan ƙananan hukumomi 774 na ƙasar.

    Shugaban kwamitin majalisar dattawa kan makarantun gaba da sakandire da TETFUND, Mohammed Dandutse, ya bayyana hakan yayin da yake sa ido kan yadda jarrabawar UTME ta 2025 ke gudana.

  16. Hotunan ɓarnar da sabbin hare-haren Isra'ila a Gaza suka haddasa

    Ga wasu hotuna da ke nuna sabon ɓarna a Gaza bayya sabbin hare-haren da Isra'ila da ƙaddamar.

    Sabbin hare-haren dai ya hallaka rayuka fiye da mutum 40 in ji majiyoyin asibitoci, inda rahotanni suka ce an kai aƙalla gawar mutum 36 asibitoci a kudu.

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    ...

    Asalin hoton, Reuters

  17. Burinmu shi ne kwantar da rikici ba tayar da shi ba - Trump

    tt

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Trump ya shaida wa dakarun Amurka a babban sansanin sojin ƙasar da ke Gabas ta Tsakiya, cewa babban abin da ya sa a gaba shi ne kwantar da rikici ba tayar da shi ba.

    Ziyarar da ya kai sansanin sojin Amurka na Al Udeid Air da ke yankin sahara a kudu maso yammcin birnin Doha, wani ɓangare ne na ziyarar kwana huɗu da yake yi a yankin Gulf.

    Tun da farko a lokacin ganawa da jagorori kasuwanci a Qatar, Trump ya ce ziyara tasa zuwa yankin za ta taimaka wajen ƙulla yerjejeniyoyin kasuwanci da Amurka, da ta kai aƙalla dala tiriliyan huɗu.

    Ana sa ran shugaban zai ƙare ziyarar tasa a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.

  18. Jirage marasa matuƙa sun canza salon yaƙin Sudan

    Jirage marasa matuƙa

    Asalin hoton, Getty Images

    Dakarun RSF a Sudan sun ƙaddamar da sabon salo a yaƙin basasar da suke yi da gwamnatin ƙasar makonni kaɗan bayan da sojojin gwamnati suka ce sun karɓe birnin Khartoum.

    RSF daga bisani ta kai hare-hare da jiragen yaƙi marasa matuƙi da ba a taɓa gani ba a birnin Port Sudan da ke gabashin ƙasar wanda a baya ake ɗauka a matsayin wuri mai zaman lafiya.

    Waɗannan hare-hare sun haddasa katsewar wutar lantarki da ƙarancin ruwa.

    Amfani da jiragen yaƙi marasa matuƙa na ƙaruwa a rikicin da ake yi tsakanin gwamnatin ƙasar da dakarun RSF, inda duka ɓangarorin biyu ke amfani da su.

    Hare-haren da aka kai kan muhimman ababen more rayuwa, ciki har da tasoshin wutar lantarki guda uku a Omdurman a ranar Laraba, sun ƙara taɓarɓare rayuwa a yankin babban birnin.

    Sauya salon da RSF ɗin na nuni da ƙudirinta na ci gaba da yaƙi, kuma yana ƙara bayyanar da yadda amfani da jiragen yaƙi marasa matuƙi ke ƙara faɗaɗa a nahiyar Afirka.

    Wannan yaƙin basasar, wanda a ke ta fama da shi har tsawon shekarara uku, ya jefa ƙasar cikin mafi munin rikicin jin kai a duniya, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

  19. Zelensky ya isa Turkiyya domin tattaunawa da shugaba Erdogan

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya isa babban birnin Turkiyya, Ankara, domin tattaunawa da Shugaba Recep Tayyip Erdogan.

    Sojojin Turkiyya ne suka tarbe shi a filin jirgin sama na Esenboga bayan ya sauka daga jirgi

    Ana tsammanin za a gudanar da ganawa tsakanin Zelensky da Erdogan cikin awa guda.

    Bayan sauka daga jirginsa, Zelensky ya yi jawabi gajere inda ya ce Ukraine na cikin ganawa da tawagar Amurka game da tattaunawa da Rasha.

    Zelensky ya ƙara da cewa Ukraine za ta yanke shawarar matakanta na gaba bayan ya gana da Shugaba Erdogan na Turkiyya.

  20. Kusan dukkan al’ummar Gaza sun rasa matsugunansu - MDD

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce aƙalla mutane miliyan 1.9 – wanda ya kai kusan kashi 90 cikin 100 na yawan jal'ummar Gaza – sun rasa matsugunansu tun bayan fara yakin.

    Da dama daga cikin su sun tsere zuwa kudancin Gaza a farkon rikicin, bayan da rundunar sojin Isra’ila ta umarce su da su bar arewacin yankin. Sai dai tun daga lokacin, wuraren da Isra’ila ke ba da umarnin ficewa daga su sun ci gaba da sauyawa akai-akai.

    Hukumar Majalisar Dinkin Duniya da ke kula da 'yan gudun hijirar Falasdinawa (UNRWA) ta ce da dama daga cikin waɗanda aka tilasta wa barin gidajensu sun kasance suna yin hijira sau da dama – wasu har sau 10 ko fiye da haka ma.

    Ta kuma ƙiyasta cewa tun daga ranar 18 ga Maris, lokacin da Isra’ila ta kawo ƙarshen zaman lafiya na watanni biyu ta kuma dawo da hare-haren ta a Gaza, aƙalla mutum 430,000 ne hare-haren ya sake tilasta wa yin hijira.