window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya. 29/10/2024

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Annur Muhammad, Isiyaku Muhammed, Umar Mikail da Ahmad Bawage

  1. Ƴan sanda a Kano sun kama ƙasurgumin ɗandaba Gundura

    Kano

    Asalin hoton, Abdullahi Kiyawa/Facebook

    Rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta ce ta kama wani ƙasurgumin ɗandaba da ake nema ruwa a jallo mai suna Inuwa Zakari wanda aka fi sani da Gundura.

    Wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ya ce an kuma samu nasarar kama wasu ɓata-gari 14 waɗanda ake zargi da aikata laifuka daban-daban a samamen da suka yi ranakun 25 da 27 ga watan Oktoba.

    Kiyawa ya ce ɗandaban ya addabi al'ummar kwaryar birnin Kano saboda irin laifuka da yake aikatawa.

    "Ya kuma kasance wanda ya haɗa baki da wasu wajen kai hari kan kwamandan ƴan bijilanti har suka raunata shi ta hanyar cire masa hannu, da kuma lalata motar ƴan sanda a wani lamari na daban," in ji Kiyawa.

    Kakakin ƴan sandan ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan waɗanda ake zargin a sashen binciken manyan laifuka na rundunar, inda daga bisani za a tura su zuwa kotu domin su fuskanci hukunci.

    Ya ce rundunar ba za ta lamunci ayyukan ƴandaba ba da kuma aikata sauran laifuka a jihar.

  2. Biden ya tattauna da Tinubu kan buƙatar sakin ma'aikacin Binance

    Biden and Tinubu

    Asalin hoton, Presidency/GettyImages

    Shugaba Bola Tinubu ya tattauna da takwaransa na Amurka Joe Biden ta wayar tarho.

    Tattaunawar da aka yi a yau Talata, ta ta'allaka ne kan wani ma'aikacin Binance mai suna Tigran Gambarayan da aka kama da laifin halasta kuɗin haram.

    Wata sanarwar da fadar White House ta fitar, ta ce shugabannin ƙasashen biyu sun kuma tattatauna kan karfafa hukumomin tsaro da kuma buƙatar sakin ɗaya daga cikin ma'aikacin kamfanin hada-hadar kuɗin kirifto.

    "Shugaba Tinubu ya kuma gode wa Amurka bisa haɗin gwiwa a fannoni daban-daban musamman ma tsaro a Afrika da kuma Afrika ta yamma baki-ɗaya," in ji sanarwar.

    Shugaba Biden ya tabbatar wa Tinubu cewa haɗin gwiwar ƙasashen za ta ci gaba da wanzuwa saboda makomar duniya ta dogara kan Afrika, don haka tana da muhimmanci.

    Sun kuma tattauna kan buƙatar bai wa Afrika kujerar dindindin a kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya.

    Biden ya kuma yi amfani da damar wajen jajantawa Najeriya kan afkuwar iftila'in ambaliya da ya faru a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

  3. Sabuwar dokar Isra'ila da ta hana ayyukan Unrwa za ta yi wa ƴan Gaza illa - MDD

    Gaza

    Asalin hoton, Getty Images

    Sakatare-janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres, ya ce sabuwar dokar Isra'ila da ta hana hukumar kula da Falasɗinawa 'yan gudun hijira gudanar da ayyukanta a Gaza, za ta yi mummunar illa ga Falasɗinawa.

    Cikin wata wasika da ya aike wa Firaiminista Benjamin Netanyahu, Guterres ya ce dokar ta janyo tashin batutuwa a ɓangaren dokokin ƙasa da ƙasa.

    Ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta ce hukumar na taka muhimmiyar rawa a Gaza.

    Tun da farko shugaban hukumar a Gaza, ya shaida wa BBC cewa, zai yi wuya su ci gaba da aiki a can, muddin Isra'ila ta tabbatar da haramcin da ta yi wa hukumar na dakatar da ayyukanta.

    Ya ce suna da makarantu 300 a Gaza sannan kusan 100 daga cikinsu a yanzu duk sun koma mafaka.

    "Muna da dubban mutane da ke samun mafaka a waɗanann wurare a karkashin tutar MDD, to idan har aka ɗauke tutar da ke kare waɗannan gine-gine ko shakka babu wani batun kariya," in ji shi.

  4. Muna kira ga gwamnatin tarayya ta ayyana dokar ta-ɓaci kan lantarki - ACF

    Lantarki

    Asalin hoton, Getty Images

    Kungiyar tuntubar juna ta dattawan arewacin Najeriya, ACF ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ayyana dokar ta-ɓaci kan ɓangaren wutar lantarki a daidai lokacin da yankin arewacin ƙasar ke ci gaba da kasancewa cikin duhu sakamakon rashin wuta.

    Wata sanarwa da jami'in hulɗa da jama'a na ƙasa na ƙungiyar, Tukur Muhammad-Baba ya fitar, ta yi zargin cewa dagan-gan gwamnati ta banzatar da harkar lantarki a yankin domin ƙara jefa harkokin kasuwanci cikin matsi.

    ACF ta bayyana mamakin cewa me ya sa arewa wadda ke samar da wutar lantarki mai yawa a ƙasar, amma kuma a ke kasawa a ba ta kaɗan.

    "Cikin mako ɗaya da ya gabata, sassan jihohin arewacin Najeriya da dama na fuskantar matsalar rashin wutar lantarki, abin da ya janyo harkokin kasuwanci da na yau da kullum suka kusa durkushewa, ga kuma ƙaruwar ɓacin-rai tsakanin al'umma," in ji ƙungiyar.

    ACF ta ce abin yana tayar da hankali matuka duba da irin sanarwa da kamfanin rarraba wutar lantarki a Najeriya (TCN) ya fitar cewa za a ci gaba da fuskantar matsalar saboda matsalolin tsaro da ake fama da su.

    Ta ce bai kamata a ce jihar Legas kaɗai tana da ƙananan tashoshin samar da lantarki har guda takwas ba yayin da ɗaukacin jihohin arewa, waɗanda ke da sama da rabin al'ummar Najeriya ke da tashoshi guda uku kaɗai a Jos da Kaduna da kuma Kano.

    Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa lamarin babbar barazana ce ga tsaron ƙasar.

    Don haka ta yi kira ga gwamnatin tarayya da sauran hukumomi da abin ya shafa da su gaggauta ayyana dokar ta-ɓaci kan matslar ta rashin lantarki, kafin matsalar ra rikiɗe zuwa tashin hankali.

  5. Tankokin Isra'ila na ci gaba da dannawa kudancin Lebanon

    Lebanon

    Asalin hoton, Reuters

    Kamfanin dillancin labaran ƙasar Lebanon (NNA) ya ruwaito cewa tankokin yaƙin Isra'ila sun danna zuwa wajen ƙauyen Khiam.

    Hakan ya nuna yadda Isra'ilar ke ƙara matsawa zuwa kudancin Lebanon tun bayan kaddamar da farmak ta ƙasa a watan da ya gabata, a cewar NNA.

    Jaridar ta ruwaito cewa tankoki da dama mallakin Isra'ila sun shiga ƙauyen Khiam da ke gabashin ƙasar.

    Isra'ila ba ta ce uffan kan haka ba zuwa yanzu.

    Hezbollah ta ce ta far wa dakarun Isra'ila da ke kudu da kuma kudu maso yammacin Khiam a ranar Talata, ta hanyar harba musu rokoki da kuma maƙaman atilari.

    Ta yi iƙirarin cewa har yanzu sojojin Isra'ila ba su karɓi iko da wani ƙauye ba a Lebanon.

  6. Libya za ta kalubalanci hukuncin CAF da ya shafi wasansu da Najeriya

    Libya

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar ƙwallon ƙafa ta Libya (LFF) za ta ce za ta ɗaukaka ƙara yayin da take ƙoƙarin soke takunkumin da aka ƙaƙaba mata bayan da aka soke wasan da ƴan wasan ƙasar za su buga da Najeriya a gasar neman shiga gasar cin kofin Afrika a 2025.

    Tawagar Super Eagles dai ta ƙi buga wasan ne da aka shirya fafatawa a birnin Benghazi bayan an karkatar da jirginsu zuwa wani filin saukar jiragen sama na daban daga wanda aka tsara za su sauka, aka kuma jibge ƴan wasan a nan ba tare da wani bayani ba har na tsawon kusan sa'o'i 16.

    Bayan haka ne kwamitin ladabtarwa na hukumar Caf ya baiwa Najeriya nasara da ci 3-0 sannan ta ci hukumar LFF tarar dala 50,000.

    Muƙaddashin shugaban LFF Abdunnaser Ahmed ya shaida wa BBC cewa "Ba za a iya ba da makin wasa ta haka ba."

  7. Za a daina dogayen layuka idan ƴan kasuwa suka fara sayen man mu - Dangote

    NNPCL

    Asalin hoton, NNPCL/X

    Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya ce za a daina samun dogayen layuka a gidajen mai muddin dillalan mai suka fara sayen mai a matatarsa.

    Dangote ya bayyana haka ne bayan wata ganawa da shugaba Bola Tinubu a yau Talata.

    Hamshaƙin attajirin na Afrika ya kuma buƙaci babban kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL, da kuma ƴan kasuwa a faɗin ƙasar da su daina shigo da mai daga waje.

    Ya ce matatarsa ita ce mafita ga batun dogayen layuka da ake samu a gidajen mai da ke faɗin ƙasar.

    "Kiyasin da na yi ya nuna cewa fetur da za mu iya sha a kullu yaumin zai kai lita miliyan 30-32, za mu iya fara bayar da wannan ko a mako mai zuwa. Ba wani abun damuwa bane saboda muna da lita miliyan 500 a tankokinmu yanzu haka. Don haka ko ba a shigo da mai cikin ƙasa ba, za a iya amfani da man mu a faɗin ƙasar har na tsawon kwanaki 12," in ji Dangote.

    Hakan na zuwa ne ƙasa da wata ɗaya bayan da gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da tsarin sayar da ɗanyen man fetur a naira ga Dangote maimakon kuɗin dala.

    Gwamnatin tarayya ta ce matakin zai daidaita farashin man fetur a ƙasar da kuma karfafa kuɗin naira ta hanyar rage buƙatar amfani da dala wajen hada-hadar ɗanyen man fetur.

  8. Rasha ta ce dakarunta sun kwace garin Selidove a Ukraine

    Ma'aikatar tsaron Rasha ta ce dakarunta sun kwace garin Selidove da ke gabashin Ukraine.

    Rundunar sojin Ukraine ba ta ce komai ba a kan iƙirarin, tana cewa a baya-bayan nan sojojinta na mayarwa da Rasha martani a hare-haren da ta ke kai wa a ciki da wajen garin.

    Selidove gari ne da ake haƙar kwal, kuma yana da nisan kilomita 17 daga kudu maso gabashin garin Pokrovsk, inda Rasha ta mayar da hankali wajen kai hare-hare a baya-bayan nan.

    Rasha ta kwace yankuna masu muhimmnaci a cikin ƴan watannin nan saboda fin karfin Ukraine da ta yi a yawan sojoji.

  9. Labarai da dumi-dumi, Gwamnatin Kano ta amince da biyan N71,000 mafi ƙanƙantar albashi

    Abba Kabir Yusuf

    Asalin hoton, Abba Kabir Yusuf/X

    Gwamnatin jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta ce ta daddale naira 71,000 a matsayin albashi mafi ƙanƙanta da za ta biya ma'aikatanta.

    Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan a fadar gwamnatin jihar ranar Talata bayan ganawa da wakilan ƙungiyar ƙwadago.

    Wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ta ce ƙarin zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Nuwamban 2024.

    Kano ta zama ɗaya daga cikin jihohin da suka amince da biyan sama da abin da gwamnatin tarayya ta amince na N70,000 tun a watan Yuli.

    Jihohin Legas da Rivers ne kan gaba bayan sun amince da N85,000, sai kuma Neja da ta ce za ta biya N80,000.

  10. Sabbin mitocin kama BBC Hausa a rediyo daga 27 Okotoba 2024 zuwa 29 Maris 2025

    ..

    Kamar yadda abokan hulɗarmu suka sani cewa agogon GMT na sauyawa a duk ranar 27 ta watan Oktoban kowacce shekara, haka ma lokacin kama tashoshin namu suke sauyawa - sakamakon ƙarewar yanayin bazara da kuma shigar hunturu.

    Ga sabon jadawalin yadda za a rinƙa kama shirye-shiryen namu a kullum daga ranar 27 ga watan Okotoban 2024 zuwa 29 na Maris 2025.

    • Shirin safe: za a kama shi a kan mita 49 ko kuma 41
    • Shirin Hantsi: Za a kama shi a kan mita 31 ko 25.
    • Shirin rana: Za a same mu a kan mita 13 da 11.
    • Shirin yamma: Za a same a kan mita 31 da 25.

    Da fatan za ku kasance da sashen Hausa na BBC a koyaushe.

  11. Abin da ya kawo jinkirin gyara lantarkin Arewa - TCN

    Trken lantarki

    Asalin hoton, TCN

    Kamfanin rarraba wutar lantarki na Najeriya ya bayyana cewa aikin gyara layin samar da lantarki na Apir-Ugaji ya ɗauki tsawon lokaci ba a kammala ba ne saboda matsalar tsaro a yankin.

    Da yake magana a wani taron manema labarai a yau Talata, Manajan Darektan, kamfanin Injiniya Abdulaziz Sule, ya ce injiniyoyin da ke gyaran suna aiki ne bisa kulawar jami'an tsaro -sojoji, kuma da zarar ƙarfe 6 na yamma ya yi dole ne su bar wajen su je wajen da babu matsalar tsaro su kwana sannan da safe su koma bakin aiki.

    Amma duk da haka ya ce, za a kammala aikin a cikin kwana biyu ko uku a hanyar wadda take da wani layin na samar da lantarki ga Kano da sauran manyan birane a arewacin Najeriya.

    Shugaban ya kuma ce shi ma layin na biyu wanda aka lalata wajen turakuna biyar nasa zai dawo bakin aiki aƙalla zuwa ranar Lahadi - cikin kwana biyar kenan.

    Injiniya Sule ya ƙara da cewa da zarar an kammala gyaran layukan biyu, za a iya aikawa da wutar lantarkin da aƙalla ta kai yawan megawatt 500 zuwa 600 ga yankin arewacin Najeriyar.

    A kan abin da kamfanin yake yi kuma don hana ɓarnata kayan samar da wutar lantarkin, ya ce suna haɗa kai da al'ummomin yankunan, inda har ma suna ba su kuɗin sufuri da kuma waya don sheda msu duk wani abu da suka gani da zai yi illa ga layukan samar da wutar.

    Sannan ya ce suna kuma haɗa kai da jami'an tsaro - sojoji da 'yansanda da rundunar tsaro da kai ɗauki (Civil_Defense...), domin tabbatar da ganin suna sintiri a wuraren kayan samar da lantarkin.

  12. Harin Isra'ila ya kashe Falasɗinawa sama da 90 a Beit Lahia da ke Gaza

    Wani hari da ya rusa gida

    Asalin hoton, reuter

    Ma'aikatar lafiyada Hamas ke gudanarwa a Gaza ta ce wani hari ta sama da Isra'ila ta kai arewacin garin Beit Lahiya ya kashe Falasdinawa aƙalla 93.

    Ma'aikatar ta ce har kawo yanzu kuma ba a kai ga gano wasu mutum 40 ba waɗanda suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan wani dogon gini da ya rushe.

    Wakiliyar BBC ta ce hotunan wajen da aka ɗauka sun nuna yadda aka naɗe gawarwakin mutane da bargo wajen wani gini mai hawa huɗu da harin ya rusa.

    Rahotanni sun ce waɗanda harin ya rutsa da su sun haɗa da mutanen da yaƙi ya raba da muhallansu ciki har da mata da yara.

    Sabon lugudan wutar da Isra'ila ke yi a arewacin Gaza ya kashe ɗaruruwan mutane abin da ya ƙara jan hankalin ƙasashen duniya wajen gargaɗin Isra'ila a kan ta yi duk abin da ya kamata wajen kare fararen hula a hare-harenta.

  13. Fadar Fafaroma ta buƙaci samun sabuwar hanyar korar limaman coci da ke lalata da yara

    Fafaroma da wani babban limami a fadarsa

    Asalin hoton, AFP

    Sabuwar hukumar kare haƙƙin yara da Fafaroma Francis ya kafa ta ce akwai buƙatar a samu wata hanyar da ta fi dacewa wajen raba cocin da limaman da aka samu fiye da sau ɗaya da laifin lalata da yara.

    Hukumar ta bayar da shawarar kafa kwamitin ladabtarwa wajen ɗaukar wasu matakai a kan abin da ta kira hanyar da ta fi dacewa wajen sanya limaman barin aiki ko kuma cire su daga mukamansu.

    Haka kuma hukumar ta ce akwai buƙatar a haɗa da samar da manufofi da tsare-tsare na bai-ɗaya wajen biyan diyya ga waɗanda aka ci zarafi.

    A makon da ya gabata ne aka kammala taron ƙoli na manyan limaman cocin, inda suka bayar da haƙuri kan abin da suka kira aƙubar da waɗanda malaman cocin suka ci zarafinsu ta lalata suke sha.

  14. Ana yawan fyaɗe a yaƙin Sudan - MDD

    Wata mata

    Wani binciken Majalisar Ɗinkin Duniya ya gano cewa fyaɗe ya yawaita a yaƙin da ake yi a Sudan inda ake zargin dakarun ƙungiyar RSF da aikatawa.

    Binciken ya gano cewa dakarun RSF na garkuwa da mata da yara aƙalla waɗanda shekarunsu suka fara daga takwas inda suke mayar da su ƙwarƙwara.

    An gano yadda ake yi wa maza da mata fyaɗe sosai a cikin binciken.

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce dukkan ɓangarorin biyu na sojojin Sudan da dakarun RSF na amfani da cin zarafin ta hanyar lalata wajen tsoratar da fararen hular da suke zargi na da alaka da maƙiyansu.

    Daga bisani binciken ya buƙaci a tura dakaru na musamman Sudan ɗin domi kare fararen hula.

  15. Majalisar Dattawan Najeriya ta ɗage zaman tantance sababbin ministoci

    Hotunan sababbin ministocin Tinubu

    Majalisar Dattawan Najeriya ta ɗage zaman da ta shirya yi a yau Talata na tantance sababbin ministocin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaɓa, zuwa gobe Laraba 30 ga watan Oktoba, 2024, da ƙarfe 12 na rana.

    Tashar talabishin ta Channels ta ruwaito cewa, majalisar ta matsar da zaman zuwa gobe ne domin bayar da dama ga waɗanda za ta tantance ɗin su kammala dukkanin ayyukan shigar da takardunsu wajen rijista da kuma shirya wa aikin tantancewar.

    Mutane bakwai ne shugaban ƙasar ya zaɓa domin naɗa su a matsayin sababbin ministocin, waɗanda ya aika da sunayensu bayan da hukumar 'yansandan farin-kaya ta DSS ta wanke su bayan gudanar da bincike a kansu.

    Mutanen bakwai su ne: Bianca Odimegwu Ojukwu - wadda tsohuwar matar jagoran Biyafara Chukwuemeka Ojukwu ce - ƙaramar ministar harkokin waje, Jumoke Oduwole ministar kasuwanci da zuba jari.

    Sauran su ne: Nentawe Yilwatda ministan ayyukan jinƙai da rage talauci, Muhammadu Maigari Dingyaɗi ministan ƙwadago, Idi Mukhtar Maiha ministan kula da dabbobi, Yusuf Abdullahi Ata ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Suwaiba Said Ahmad ministar Ilimi.

    Shugaba Tinubu ya zaɓi sababbin ministocin bakwai ne bayan sallamar wasu guda shida, a wani garambawul da ya yi wa majalisar zartarwarsa a makon da ya gabata.

  16. Za mu janye yajin aiki ne kawai idan an biya mu kuɗaɗenmu –SSANU

    SSANU da NASU

    Shugaban ƙungiyar manyan ma'aikatan jami'o'in Najeriya, Mohammed Ibrahim, ya ce ƙungiyar za ta janye yajin aikin da ta tsunduma ne kawai idan an biya mambobinta albashin da suke bi bashi.

    Ibrahim ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da tashar talabijin ta Channels a jiya Litinin, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Ƙungiyar ta SSANU, ta shiga yajin aikin sai-baba-ta-gani ne, daga ranar Lahadi da daddare, saboda rashin biyan mambobinta albashinsu na wata huɗu.

    Shugaban ƙungiyar ya ce, albashin nasuya maƙale ne a ma'aikatar kuɗi kuma sai an biya su kafin su koma aiki.

    Ibrahim ya ce a yanzu sun samu tabbacin ganawa da ministoci huɗu kan batun da wasu matsaloli, inda za su gana da su cikin makon nan.

  17. An kori tare da tsare ɗansandan da ya kashe mawaƙi a jihar Enugu

    'Yansandan Najeriya

    Asalin hoton, OTHERS

    Rundunar 'yansandan Najeriya ta ce ta gurfanar da jami'inta, Sufeto Joseph Ozonwanji da ake zargi da kashe wani mawaƙi a jihar Enugu, gaban shari'a.

    A sanarwar da ta fitar rundunar ta ce a yanzu jami'in wanda a da yake aiki a rundunar yaƙi da ƙungiyoyin asiri a jihar yana tsare a gidan yari bisa tuhumarsa da laifin kisan mawaƙi Okezie Nwamba, wanda aka fi sani da Igbo-Jah.

    A jiya Litinin ne aka gurfanar da ɗansandan a gaban kotun majistare ta Enugu ta gabas.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kai ga tuhuma tare da gufanar da jami'in ɗansandan ne bayan da hukumar 'yansanda ta yi bincike a kansa ta kuma same shi da laifi sannan ta kore shi daga aiki

    Ozonwanji was arraigned on Monday on one count charge bordering on murder before a Chief istrative Magistrate, Enugu East Magistrate Court,

    Bayan gabatar da tuhumar a kotun, Majistare Ngozi Edean, ta umarci sashen gabatar da ƙara ya bayar da shawara kan shari'ar shi kuma wanda ake tuhumar ya yi zaman waƙafi.

    Ana tuhumar Ozonwanji ne da kisan Nwamba ta hanyar harbinsa da bindiga, AK47.

  18. Hezbollah ta naɗa sabon shugabanta

    Naim Qassem

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Kafin naɗin, Sheikh Naim Qasim shi ne mataimakin babban sakatarenta

    Ƙungiyar Hezbollah ta naɗa Naim Qassem a matsayin sabon shugabanta, inda ta kai shi wannan matsayin daga muƙamin mataimakin babban sakatarenta.

    Qassem zai maye gurbin daɗaɗɗen shugabanta Hassan Nasrallah, wanda Isra'ila ta kashe a wani harin bam a Beirut a watan da ya wuce na Satumba.

    Sabon shugaban ya kasance ɗaya daga cikin jagororinta da suka rage a raye bayan da Isra'ila ta kashe yawancinsu a hare-hare a makonnin nan.

    Yanzu dai ba a san inda yake zaune ba, yayin da wasu rahotanni ke cewa yana Iran, wadda ke taimaka wa Kungiyar.

    A sanarwar da ta fitar ta naɗin nasa ƙungiyar ta ce ta yi hakan ne bisa dogaro da Allah (SWT) tare da bin tsari na Musulunci, da bin ƙa'idar manufofinta, da sharuɗanta na zaɓe.

    Ƙungiyar ta yi fatan Allah Ya yi masa jagoranci, tare da alƙawarin biyayya ga Allah, da martaba ruhin babban jagoranta babban shahidi Sayyid Hassan Nasrallah da sauran shadidan da ta ce sun rasu.

    Sannan ta lashi takobin ci gaba da gwagwarmayarta har sai ta kai ga nasara.

  19. Sojojin Najeriya sun ce sun kashe 'yan Boko Haram da dama a Borno

    Boko Haram

    Asalin hoton, NAF

    Rundunar sojin saman Najeriya ta ce jiragen samanta sun kashe mayaƙan Boko Haram da dama a ranar 25 ga Oktoba a arin Bula Marwa a Borno.

    Daraktan hulɗa da jama'a na rundunar, Iya Comodore, Olusola Akinboyewa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin a Abuja.

    Akinboyewa ya ce sun gano Bula Marwa ne garin da Boko Haram suka taruwa, inda suka gano babura suna ta zirga-zirga, hakan ya sa aka aika jiragen sama yankin, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN ya ruwaito.

    "Da isan jiragen, sai hoton da jiragen ya ɗauko ya tabbatar da taron ƴan Boko Haram a saman babura 12, inda aka bibiyi baburan zuwa wani wuri da akwai ƙarin ƴan ta'addan suke jiran zuwan su.

    "Wannan ya sa jiragen suka yi ɓarin wuta a yankin, sannan daga baya jirgin ya hango ƴan ta'addan suna sake dawowa yankin domin kwashe waɗanda suka raunata.

    "Wannan ya sa jiragen suka koma, suka ƙara yin luguden wuta, inda a nan ma aka sake kashe wasu ƴan ta'addan."

    Akinboyewa ya ce an sake ganin wasu tarin ƴan Boko Haram sun taru a ƙarƙashin wata bishiya, inda nan ma jiragen suka ƙara bin su, suka musu ɓarin wuta.

  20. Isra'ila ta hana ayyukan hukumar jinƙai ta Unrwa a Gaza

    Unrwa

    Asalin hoton, Reuters

    Majalisar Isra'ila ta kaɗa ƙuri'a a daren jiya, inda ta haramta ayyukan hukumar kula da Falasɗinawa ƴan gudun hijira (Unrwa) a yankin gabashin Jeruselam da ta mamaye nan da wata uku.

    Haka kuma ta haramta wata alaƙa tsakanin hukumar da jami'an Isra'ila, wanda haken ke nufin jami'an ayyukan jinƙan ba su da wata kariya a Isra'ila, sannan an kulle hedwatarta da ke gabashin Jerusalem.

    Sai dai ana ganin wannan matakin zai matuƙar kawo tsaiko ga ayyukan hukumar, musamman a Gaza da gaɓar yamma da tekun Jordan.

    Yuli Edelstein, shugaban kwamitin tsaro da harkokin waje na majalisar Isra'ila ya zargi Unrwa da "alaƙa da mai ƙarfi" da Hamas. duk da cewa ta musanta hakan, tare da cewa aikinsu kawai suke a Gaza.