window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 17/07/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail da Badamasi Abdulkadir Mukhtar

  1. An saƙo ɗan jaridan da aka kama bisa kuskure a Kenya

    ...

    Asalin hoton, Ruth Nesoba/BBC

    Ƴan sandan Kenya sun saki wani gogaggen ɗan jarida bayan da suka kama shi a ofishin ƴan sanda inda suka tumurmusa shi cikin wata mota.

    Macharia Gaitho, mai shekaru 65, ya ce wasu motoci biyu ne suka bi shi a kusa da gidansa da ke Nairobi babban birnin ƙasar a lokacin da ya ke tare da dansa mai shekaru 19, wanda ya tuka shi da shi zuwa wani ofishin ƴan sanda da ke kusa don kare lafiyarsa – inda aka jefa shi da karfi cikin mota aka yi gaba da shi.

    Daga baya ƴan sanda sun ce lamarin kuskure ne, domin sun daɗe suna farautar wani mutum da suke zargi da katsalandan cikin binciken da ƴan sanda ke yi kan wanda ake zargi da kisan kai.

    Wani bidiyo da aka yaɗa a kafafen sada zumunta ya nuna yadda jami’a sa sanye da kayan sarki suka tursasa dan jaridar cikin wata farar mota.

    Hakan ya haifar da martani mai zafi daga ƴan ƙasar ta Kenya a shafukan intanet, inda ake ta zargin jami’an tsaro da sace mutanen da ake ganin suna da alaƙa da zanga-zangar ƙin jinin gwamnati a baya-bayan nan.

  2. Tinubu ya naɗa sabuwar shugabar ma'aikatan Gwamnatin Tarayya

    Didi Esther Walson-Jack

    Asalin hoton, STATE HOUSE

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da naɗin Misis Didi Esther Walson-Jack, OON, a matsayin sabuwar shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya, daga ranar 14 ga Agusta, 2024.

    Wata sanarwar da ta fito daga ofishin mai magana da yawun shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale, ta bayana cewa Misis Walson-Jack za ta karɓi aiki ne daga Dr. Folasade Yemi-Esan, CFR wadda za ta yi ritaya a ranar 13, ga watan Augustan wannan shekarar.

    An naɗa Misis Walson-Jack a matsayin Babbar Sakatariya ta Tarayya a 2017 kuma ta yi aiki a ma'aikatu da dama.

    Sanarwar ta ƙara da cewa, yayin da Shugaba Tinubu ke miƙa godiyarsa ga shugabar ma’aikata mai barin gado, ya yi kira ga shugabar ma’aikata mai jiran gado da ta gudanar da aikinta cikin gaskiya da aminci kuma ta tabbatar da bin tsare-tsare da dokokin aikin gwamnati.

  3. Masana sun gano hanyar ƙara wa ɓeraye tsawon rai - za a gwada kan ɗan'adam

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wata tawagar bincike ta ƙasa da ƙasa ta gano cewa toshe kumburin ɓangarorin jikin beraye na iya tsawaita rayuwarsu da kusan kashi ashirin da biyar cikin ɗari, a wani bincike da suke fatan shi ma zai samu fa'ida ga ɗan'adam.

    Masana kimiyyar sun daƙile haɓakar sinadarin da aka sani da interleukin-11 a cikin ɓerayen da aka killace a ɗakin gwaje-gwaje.

    Waɗannan ɓeraye ba tsawon rai kawai suka ƙara ba, amma sun nuna ƙoshin lafiya, tare da ingantaccen aikin tsokar jiki da sheƙin gashi da kuma rashin yiwuwar kamuwa da cutar kansa yayin da suke ƙara tsufa.

    Ana gwada irin wannan maganin a kan mutane, amma ba a san ko zai yi irin tasirin da aka gani a jikin ɓerayen ba.

  4. Muna goyon bayan ƴan ƙwadago kan ƙarin albashi - Gwamnonin PDP

    ...

    Asalin hoton, PDP NIGERIA/FACEBOOK

    Gwamnonin Najeriya waɗanda aka zaɓa a ƙarƙashin inuwar Jam'iyyar PDP sun bayyana goyon bayansu ga ƙungiyar ƙawadago ta ƙasa a yunƙurin da take yi na ganin gwamnatin Najeriya ta yi ƙari a albashin ma'aikatan ƙasar mafi ƙanƙanta.

    Gwamnonin sun bayyana haka ne a sanarwar ƙarshen taro da suka fitar a bayan taron su na ƙasa da suka gudanar a jihar Enugu, da ke kudu maso gabashin Najeriya.

    Yayin da suka koka kan tafiyar hawainiyar da tattaunawar gwamnati da ƙungiyar ƙwadago ke yi, gwamnonin sun yi la'akari da cewa matsayar da ƙungiyar ta ɗauka ya dace a halin yanzu ganin irin wahalhalun da ƴan Najeriya ke ciki sakamakon tsadar rayuwa da ake fama da ita.

    Sanarwar ta ƙara da cewa ''Yayin da taron gwamnonin ke goyon bayan buƙatar ƙungiyar ƙwadago, dole ne duk wata yarjejeniya ta yi la’akari da albashin da gwamnatocin ƙananan hukumomi da na jihohi za su iya biya''.

    ''Yayin da ake ci gaba da tattaunawa, muna kira ga dukkan ɓangarori da su kai zuciya nesa, kar a kai ga furuci da kuma ayyukan da za su iya haifar da karya doka, wanda ka iya kai wa ga jefa tattalin arziƙi cikin ruɗani.''

    Gwamnonin na PDP sun kuma bayyana takaici kan "yadda tsare-tsaren gwamnatin tarayya ƙarƙashin jam’iyyar APC ke neman gurgunta tartalin arzikin ƙasar."

  5. Zulum ya roki ƴan Najeriya su ƙaurace wa zanga-zanga

    ...

    Asalin hoton, X/BornoGov

    Gwamna jihar Borno, Babagana Zulum ya yi kira ga al'ummar jihar da ma ƴan Najeriya baki ɗaya da su guje wa shiga zanga-zangar da ake shirin yi a faɗin ƙasar nan a wata mai zuwa.

    Zulum ya yi wannan kira ne yayin wani taron masu ruwa da tsaki a gidan gwamnati da ke Maiduguri a ranar Laraba.

    Ya ci gaba da cewa su yi yunƙurin shiga tattaunawa mai ma’ana domin zanga-zangar na iya haifar da tarzoma da tahin hankali.

    Ya yi nuni da cewa har yanzu jihar ba ta farfaɗo daga rigingimun masu tayar da ƙayar bayan da ta kwashe shekara 13 tana fama da su ba, yana mai cewa zanga-zangar ba za ta kasance hanya mafi inganci na tabbatar zaman lafiya mai ɗorewa a jihar ba.

    ''Mu shiga tattaunawa mai ma'ana, gwamnatin tarayya da na jihohi suna yin duk mai yiwuwa don ganin an rage wahalhalun da jama’a ke ciki a Najeriya.” in ji shi

    Ya ƙara da cewa “Na yi farin cikin ganin da yawa daga cikin masu ruwa da tsaki sun yi alƙawarin ba za su shiga zanga-zangar ba. Ina mai tabbatar muku da cewa gwamnatin jihar Borno za ta bi diddigin ganin an aiwatar da abin da abubuwan da suka gabatar.”

    Taron dai ya samu halarcin shugabannin hukumomin tsaro da sarakunan gargajiya da ƙungiyar ƴan jarida ta Najeriya da kuma ƙungiyar lauyoyin Najeriya.

  6. Tinubu ya ƙaddamar da asusun bai wa ɗalibai bashin karatu

    ...

    Asalin hoton, FB/BOLA TINUBU

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ƙaddamar da asusun baiwa dalibai bashin karatu ta Najeriya (NELFund), a wani taro d aka gudanar a zauren taro na fadar shigaban ƙasa da ke Abuja

    Taron ya sami halarcin shugabannin majalisar dokokin ƙasar, da sakataren gwamnatin tarayya, da wasu ministoci, da shugabannin hukumomi, da mambobin kwamitin da gudanarwa na asusun ƙarƙashin jagorancin shugaban kwamitin, Jim Ovia.

    A nasa ɓangaren, Shugaban asusun ta NELFund, Akintunde Sawyerr, ya ce manhajar asusun ta karbi sama da bukatu 110,000 na ɗalibai masu neman bashin karatu.

    Shirin baiwa ɗalibai bashin na neman bayar da tallafin kuɗi, wanda ya haɗa da kuɗin makaranta da na sanya wa a aljihu, ga ɗaliban da suka cancanta a duk faɗin ƙasar.

    Sama da dalibai miliyan 1.2 ne ake sa ran za su ci gajiyar zango na farko a shirin.

  7. Me ya sa Sunday Igboho ya buƙaci Fulani su fice daga jihar Oyo?

  8. Daga leburanci zuwa gasar Olympics: Rayuwar ɗan Najeriya Anuoluwapo Opeyori

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo

    Anuoluwa, wanda aka haifa a unguwar marasa galihu da ake kira Mokoko a cikin garin Legas, inda bai samu arziƙin yin wasan bton a fili mai kyawu ba, yanzu zai wakilci Najeriya a gasar Olympics.

    Shi ne matashin da ya fi kowane ɗan wasan bton a nahiyar Afirka lashe kofuna na gasa ta ƙasa da ƙasa.

    A wannan bidiyo duba yadda ya samu wannan nasara da kuma tuntuɓar mahaifiyarsa wadda ita ma ta taɓa yin wasan bton a baya.

  9. Lauyoyin Guinea sun shiga yajin aiki saboda matsin lambar sojoji

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Aiki ya tsaya cak a kotuna da ke faɗin ƙasar Guinea bayan da lauyoyi suka fara yajin aikin gama gari don nuna adawa da gwamnatin mulkin sojan da ke aiwatar da abin da suka kira kame ba bisa ka'ida ba.

    Yajin aikin dai shi ne na baya-bayan nan na nuna bacin rai dangane da kame wasu fitattun ƴan gwagwarmaya biyu da ke jagorantar yaƙin komawa kan tafarkin dimokuradiyya.

    Shugaban masu ra'ayin mazan jiya na Faransa Jean-Luc Mélenchon, wanda haɗakar jam'iyyun da ya jagoranta ta lashe mafi yawan kujeru a zaɓen ƴan majalisar dokokin ƙasar a makon jiya, ya yi kira da a sake su.

    Sojojin Guinea sun hamɓarar da shugaba Alpha Condé a shekara ta 2021, bayan zanga-zangar adawa da mulkinsa lokacin da ya lashe zaɓe karo na uku mai cike da cece-kuce.

    Ƴan ƙasar Guinea da dama sun yi maraba da juyin mulkin, amma a yanzu suna zargin sojoji da murƙushe ƴan adawa da kuma watsi da alƙawarin da suka yi na miƙa mulki ga gwamnatin dimokradiyya.

    Ƙungiyar lauyoyin ta ce lauyoyin za su Ƙauracewa zaman kotun na makonni biyu masu zuwa, har zuwa ranar 31 ga watan Yuli.

    Lauyoyin sun shirya komawa kotu a ranar 1 ga watan Agusta - kwana guda lokacin da za a yanke hukunci a shari'ar tsohon shugaban mulkin soja Dadis Camara bisa zargin cin zarafin bil'adama.

  10. Wa Ingila za ta naɗa sabon koci?

  11. Tinubu ya ƙara naira tiriliyan 6.2 a cikin kasafin kuɗin 2024

    ..

    Asalin hoton, PRESIDENCY NIGERIA

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu, ya bukaci majalisar dattawa da ta yi wa dokar kasafi ta 2024 da kuma dokar kudi ta 2023 gyaran fuska ta hanyar amincewa da ƙarin naira tiriliyan 6.2 a cikin kasafin kuɗin.

    Buƙatar ta Tinubu na ƙunshe ne a cikin wata wasiƙa da ya aika wa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, kuma aka karanta a zauren majalisa ranar Laraba.

    A cikin wasikar, Shugaban ya ce yana son ɗaukar matakin ne bisa dogaro da sashe na 58, ƙaramin sashe na biyu na kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999 da aka yi wa gyaran fuska.

    Wasiƙar ta ce “Ana buƙatar yin gyara ga ƙudirin kasafin kuɗin shekarar 2024 don samar da ƙarin naira tiriliyan 3.2 don ayyukan more rayuwa da sauran muhimman ayyuka da za a gudanar a faɗin ƙasar.

    “Da kuma naira tiriliyan uku don biyan wasu buƙatu na yau da kullum, waɗanda suka dace don gudanar da ayyukan na tafiyar da harkokin gwamnatin tarayya, waɗanda za a samu ta hanyar kuɗaɗen shigar da gwamnatin tarayyar Najeriya ke sa ran samu,”

    Tinubu ya ƙara da cewa ana buƙatar aiwatar da gyare-gyaren da ake neman yi wa dokar kuɗi ta 2023, domin a sanya haraji kan ribar da bankuna suka samu a cikin bayanan kudi na shekarar 2023.

    Ya yi bayanin cewa an yi hakan ne don samar da kuɗaɗen da za a yi amfani da su wurin bunƙasa manyan ababen more rayuwa a fannin ilimi da kiwon lafiya, da sauran ayyukan jin dadin jama'a.

  12. Gobara ta kashe mata uku ƴan'uwan juna a Kano

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Wata gobara a Kano ta yi sanadiyyar mutuwar wasu mata uku ƴan'uwan juna tare kuma da haifar da asarar dukiya.

    Gobarar wadda ta faru a daren da ya gabata ta cinye wani gida da ke ƙunshe da dangin kwamishinan ilimi na jihar ta Kano, Yusuf Kofarmata.

    A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na fesbuk, kwamishinan ya ce: "Allah Ya yi wa ƴata Maimuna (Islam), da yayata wacce nake bi, Hajiya Khadija da matar yayana, Juwariyya, rasuwa."

    Lamarin dai ya faru ne a cikin daren yau Laraba a unguwar Ƙofarmata da ke cikin birnin na Kano.

  13. Somalia ta sha alwashin ƙwato makaman da aka ƙwace a hannun jami'an tsaron ta

    Somalia

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma'aikatar harkokin cikin gidan Somalia ta sha alwashin ƙwato makamai masu ɗinbin yawa da wata ƙungiyar masu ɗauke da makamai ta ƙwace a kusa da garin Abudwaq.

    An ƙwace makaman ne a lokacin da jami'an hukumar leƙen asirin ƙasar, NISA ke ɗauke dasu a cikin manyan motocin ɗaukar kaya a ranar 15 ga watan Yuli.

    Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun ce hukumar leƙen asirin ƙasar, NISA ta shigo da makaman ne daga Habasha, kuma ƙungiyar masu ɗauke da makamai ta yi masu kwanton ɓauna, ta kuma ƙwace makaman daga hannun su.

    Ƴan bindigar sun ci galaba kan dakarun na NISA tare da kashe jami'ai 20 a faɗan da su ka gwabza.

    Ƴan bindigar sun yi iƙirarin cewa an shigo da makaman ne domin miƙa su ga sauran ƙungiyoyi masu adawa da su.

    Sai dai gwamnatin tarayyar ƙasar ta ce dakarun NISA sun ƙwace makaman ne da aka yi safara ba bisa ƙa'ida ba, bayan tattara bayanan sirri a kan yadda ake shigar da makamai ƙasar.

    Somalia na fama da matsalar yaɗuwar makamai a tsakanin al'umma, kuma bayanai na cewa ana shiga dasu ƙasar ne domin amfanin ƙungiyoyin ƴan bindiga irin su al-Shabab.

  14. An zargi ƙungiyar Hamas da aikata laifukan yaƙi

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Ƙungiyar Human Rights Watch ta ce Hamas da wasu ƙungiyoyin Falasɗinawa masu riƙe da makamai sun aikata laifukan yaƙi daban-daban a yayin harin da suka kai kudancin Isra'ila a ranar bakwai ga watan Oktoba.

    Wani sabon rahoton ƙungiyar ya zargi ɗaruruwan ƴan bindigar da suka karya dokar kan iyakar ƙasa, da aikata munanan laifuka da suka haɗa da kai hari kan fararen hula da kisan fursunonin yaƙi da cin zarafin mata ta hanyar lalata da kuma garkuwa da mutane.

    Ƙungiyar ta kuma gano cewa ''mayaƙan da suka kai harin sun tsara yin garkuwa da mutane tun da farko, ba wai sai bayan harin ne suka yi tunanin garkuwa da mutane ba''

    Hamas ta gaggauta musanta rahoton na Human Rights Watch, inda ta bayyana shi a matsayin ƙagaggen zance kuma ''ƙarya'', ta kuma nemi a nemi gafarr ta.

    Mutane aƙalla 1,200 ne aka kashe a lokacin harin, cikin su harda Isra'la

    Isra'ila ta mayar da martani ta hanyar kai hare-hare Gaza, kuma rahotanni sun ce mutane aƙalla 38,790 aka kashe a Gazar, kamar yadda hukumar lafiya ta Hamas ta sanar.

    Human Rights Watch ta ce ta tattara bayanan rahoton nata ne bayan hira da mutane 144 da suka shaida harin na ranar bakwai ga watan Oktoba, da kuma nazari a kan hotuna da bidiyo 280 da aka wallafa a shafukan sada zumunta.

  15. Ƴan adawa sun ƙaurace wa shirin gwamnatin haɗin gwiwa a Mali

    Mali

    Asalin hoton, Getty Images

    Jam'iyyun siyasar Mali sun ƙauracewa kiran hukumar zaɓe ta ƙasar, AIGE na tattaunawa domin kafa gwamnatin haɗaka da za ta mayar da mulki ga farar hula, bayan ɗage takunkumin harkokin siyasa a ƙasar.

    A cewar rahoton hukumar ta AIGE ta gayyaci masu ruwa da tsaki a harkar siyasa domin tattaunawa a ranar 15 ga watan Yuli amma kuma jam'iyyun siyasar da ke ƙarƙashin yarjejeniyar ranar 31 ga watan Maris sun ce ba za su shiga haɗakar ba, sun kuma nemi a gudanar da zaɓe domin kawo ƙarshen batun gwamnatin riƙon ƙwarya.

    Sun kuma buƙaci da a gaggauta sakin jagororin ƴan adawa 11 da aka kama a ranar 20 ga watan Yuni a kan zargin karya dokar hana taron siyasa, bayan an same su da halartar wani taro na tattauna siyasar cikin gida, tsakanin ƙungiyoyin da ke cikin yarjejniyar 31 ga watan Maris.

    Jam'iyyun siyasa tare da ƙungiyoyin fararen hula sun zargi gwamnatin sojin da goyon bayan mulkin kama karya domin neman hanyar ci gaba da riƙe mulki.

    Tun bayan ƙwace mulki a watan Yunin 2021 gwamnatin mulkin sojin da Konal Goita ke jagoranta ta riƙa gudanar da salon mulki irin na neman karya ƴan adawa.

  16. Majalisa ta tsige Ndume daga muƙaminsa kan sukar fadar shugaban ƙasa

    ...

    Asalin hoton, SenateNG

    Majalisar dattijan Najeriya ta cire sanata mai wakiltar Borno ta Kudu, Ali Ndume daga muƙamin mai tsawatarwa.

    Majalisar ta ɗauki wannan mataki ne a yau Laraba bayan ƙorafi da jam'iyyar APC, mai mulki ta yi kan wasu kalaman sanatan a baya-bayan nan.

    Shugaban majalisar, Sanata Godswill Akpabio ne ya karanto wata wasiƙar ƙorafi daga shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje da kuma sakatarenta, Sanata Bashir Ajibola.

    Wasiƙar ta zargi Sanata Ndume da furta wasu kalamai waɗanda ke iya zubar da ƙimar gwamnati da kuma karya gwiwar masu son shigowa ƙasar domin zuba jari.

    Bayan karanta wasiƙar ne Sanata Akpabio ya nemi a kaɗa ƙuri'a domin amincewa ko watsi da buƙatar kuma daga ƙarshe sanatocin suka zaɓi tsige Ndume.

    Haka nan kuma majalisar ta cire Ndume daga muƙaminsa na mataimakin shugfaban kwamitin kasafin kuɗi na majalisar.

    Majalisar ta ce a yanzu an mayar da sanatan zuwa kwamitin harkokin yawon shaƙatawa.

    Nan take kuma aka zaɓi Sanata Tahir Munguno domin maye gurbin Sanata Ali Ndume.

    Ali Ndume, sanata ne wanda ya yi ƙaurin suna wajen sukar manufofin gwamnati, yayin da magoya bayansa ke masa kallon mai faɗin albarkacin bakinsa ba tare da tsoro ba.

    Wannan dai ba shi ne karo na farko da Majalisar Dattijan Najeriyar ta dakatar da wani wakili na ta ba.

    Ko a watan Maris ɗin 2024 majalisar ta dakatar da Sanata Abdul Ningi mai wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya daga majalisar bayan zargin sa da furta "kalamai da ke iya zubar da ƙimar majalisar."

    Majalisar ta ɗauki matakin ne bayan wata tattaunawa da sanatan ya yi da kafar yada labarai ta BBC, inda ya yi zargin cushe a cikin kasafin kudin ƙasar.

  17. Gwamnonin PDP sun isa Enugu domin taron su na ƙasa

    Gwamnonin PDP

    Asalin hoton, @SenBalaMohammed

    Gwamnoni 10 daga cikin 13 na jam'iyyar PDP sun isa jihar Enugu domin taron su na ƙasa da za a yi yau Laraba.

    Gwamnonin da suka halarta kawo yanzu sun haɗa da Oluwaseyi Makinde jihar Oyo da Umo Eno na Akwa Ibom da Sheriff Oborevwori na Delta da Bala Mohammed na Bauchi da Godwin Obaseki na Edo da Caleb Mutfwang na Plateau da Agbu Kefas na Taraba da kuma Dauda Lawal na jiharZamfara.

    Sauran sun haɗa da Ahmadu Fintiri na Adamawa da Siminalayi Fubara na Rivers da kuma mai masaukin baƙi, Peter Mbah na jihar Enugu.

    Babu dai bayani a kan abin da za a tattauna a taron.

    Rahotanni sun ce ana sa ran muƙaddashin shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum da sauran jiga-jigan jam'iyyar za su halarci taron na Enugu.

    Wata majiya ta ce akwai yiyuwar batun zaɓen shugabannin jam'iyyar a matakin jihohi da za a yi ranar 27 ga watan Yuli da kuma shirin zaɓen gwamonin jihar Edo da kuma Ondo ne taron zai mayar da hankali a kai.

  18. Sarki Charles ya gabatar da tsare-tsaren sabuwar gwamnatin Birtaniya

    King Charles

    Sarki Charles ya gabatar da tsare-tsaren sabuwar gwamnatin Birtaniya a ƙarƙashin jam'iyyar Labour a taron ƙaddamar da majalisar dokoki a birnin London.

    Jawabin sarkin ya ƙunshi cikakken bayani a kan sababbin dokoki 35, ciki har da mayar da hankali kan tattalin arziki da tabbatar da tsaro a kan iyakar Birtaniya, da yaƙi da rashawa, da kuma sufurin jirgin ƙasa.

    Sarkin ya ce gwamnati za ta kawo ''sabon tsari da zai kare ma'aikata da kuma bunƙasa ƙwatar masu ƴanci''

    Ya taɓo batun inganta ayyukan samar da abubuwan more rayuwa, inda ya ce ministoci za su ƙara ƙwazo domin cimma nasarar hakan.

    Sarki Charles ya kuma yi magana kan yaƙin Isra'ila da Hamas, inda ya jaddada matsayar Birtaniya ta goyon bayan kafa ƙasashe biyu masu ƴancin kansu a yankin domin kawo ƙarshen rikicin da ake fama da shi.

  19. An sako mahaifiyar Rarara bayan mako uku da sace ta

    RARARA

    Asalin hoton, DAUDAKAHUTU/IG

    Mahaifiyar shahararren mawaƙin Hausa Dauda Kahutu Rarara, ta kuɓuta daga hannun ƴan bindiga bayan shafe mako uku a hannunsu.

    Mawaƙin ne ya tabbatar da sakin Hajiya Hauwa'u Adamu a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Instagram da safiyar yau Laraba.

    An sace dattijuwar ne ranar 28 ga watan Yuni a ƙauyen Kahutu da ke ƙaramar hukumar Danja ta jihar Katsina.

    "Cikin yarda da Amincin ubangiji, mun samu dawowar mama cikin aminci," in ji shi. "Ina matuƙar godiya ga unbangijina."

    Kawo yanzu dai babu cikakken bayani game da ko an biya kuɗin fansa kafin sakin nata.

  20. An kashe ƙarin mutum huɗu yayin zanga-zangar adawa da gwamnati a Kenya

    Kenya

    Asalin hoton, BBC/MERCY JUMA

    Wasu ƙarin mutum hudu ne ake zargin ‘yan sandan Kenya sun kashe yayin zanga-zangar adawa da gwamnatin shugaba William Ruto a jiya, wanda ya kawo adadin waɗanda suka mutu sama da 50 a cikin watan da ya gabata, kamar yadda NTV ta ruwaito.

    Mutuwar ta faru ne a gundumar Makueni, Nairobi, da Kitengela.

    Hukumar kare haƙƙin bil adama ta ƙasar Kenya ta bayar da rahoton cewa, mutum 50 ne suka mutu tun bayan fara zanga-zangar a ranar 18 ga watan Yuni.

    Muƙaddashin Sufeto Janar na 'yan sandan ƙasar Douglas Kanja ya yi gargadin yiwuwar kutsawar masu aikata muggan laifuka a zanga-zangar, lamarin da ya sa 'yan sanda suka mayar da martani mai karfi da hayaƙi me sa hawaye da barbi da harsasai.

    Mutane da dama a kananan hukumomin Nakuru da Nairobi da Mombasa da Nyeri da kuma Machakos sun jikkata.

    Ƙungiyar ‘yan jarida ta Kenya (KUJ) ta yi kira da a gudanar da bincike a kan wani dan sanda da ya harbe wani dan jarida da ke bayar da rahoto kan zanga-zangar a gundumar Nakuru.

    Duk da janye dokar ƙrin harajin da shugaba Ruto ya yi, da rage kashe kudade, da kuma rusa majalisar ministocinsa, masu zanga-zangar na ci gaba da nemansa ya yi murabus, bisa la'akari da cin hanci da rashawa da rashin shugabanci na gari.