Hikayata: Labarin Cizon Yatsa
A ci gaba da kawo muku jerin labarai 12 da alƙalan gasar Hikataya ta 2023 suka ce sun cancani yabo, a yau mun kawo labari na ƙarshe cikin jerin, mai suna Cizon Yatsa.
Labari ne da Aisha Adam, mazauniyar Kadawa, Layin Masjidul Qur’an, Bayan Sabuwar Tasha, Rijiyar Zaki, a birnin Kano, ta rubuta.
Labari ne na wata matar aure da ta tsinci Talatarta a Laraba, bayan da ta biye wa son zuciya da ruɗin ƙawa, ta yi watsi da aurenta da 'ya'yanta, ta kuma shiga neman duniya, ƙarshe dai duniyar ba ta samu ba, sai dai tarin nadama.
Nabeela Mukhtar Uba ce ta karanta labarin