'Gazawar gwamnati ke sa wasu jami'an tsaron Najeriya samar da makamai ga 'yanta'adda'

'Yanbindiga dauke da makamai

Asalin hoton, NPF

Wasu masana a kan harkokin tsaro na zargin mahukuntan Najeriya da rashin daukar kwararan matakan hukunta jami'an tsaro da ake samu da laifin safarar makamai ga 'yanbindiga da kuma rashin biyan jami'an tsaron kasar albashin da ya dace, da cewa hakan na daga abubuwan da ke janyo baragurbin jami'ai safarar makamai ga mayakan Boko Haram da 'yanfashin daji.

Barista Audu Bulama Bukarti, na daga cikin masu wannan ra'ayi kamar yadda ya bayyana a tattaunawarsa da BBC.

Lauyan kuma masanin harkokin tsaro a nahiyar Afirka, ya ce gwamnatin Najeriya na sakaci da lamuran da suka shafi tsaro da suka hada da rashin bibiyar yadda ake kashe kudade a bangaren da ma yin biris da makomar sojoji da sauran masu aikin samar da tsaro a kasar.

Ya ce muddin hakan ya ci gaba to ba ta yadda za a iya kawo matsalar tsaro da ta addabi Najeriya.

Bulama na magana ne kan rahotannin da ke cewa an kama wasu daga cikin jami'an tsaron Najeriya da ke samar da makamai ga mayakan Boko Haram da kuma 'yan fashin daji.

Ya ce : ''Gaskiya wannan babban abin takaici ne domin ba iya laifi ba ne, cin amanar kasa ne, a ce wanda aka dauka aka dankawa amana aka ba shi makaman al'umma da rigar-sarki shi yake irin wannan.''

''Suna amfani da ofishinsu ta yadda ba za a yi musu dogon bincike ba, to da wannan suke amfani suna irin wannan safarar.'' in ji shi.

Ya kara da cewa, ''su kansu jami'an gwamnati sun yi irin wannan zarge-zarge a baya, kuma wanda ya yi zargin a baya-bayan nan shi ne gwamnan jihar Borno.''

Dangane da rahoton da hukumomin kasar suka bayar na baya-bayan cewa an kama wasu jami'an sojoji suna samar da makamai ga 'ya Boko Haram da 'yanfashin daji, masanin ya ce, bincike ne zai tabbatar su waye da kuma yadda suke samun makaman.

Ya ce idan aka dubi yadda rahoton ya zo, su wadannan jami'ai su suke samar da makaman ga 'yanta'adda, ko dai ta hanyar amfani da haramtattun masu sayar da makamai, suna sayowa ta bayan fage suna kai wa 'yantaddan ko kuma satowa suke yi ta rumbun gwamnati ko kuma sata suke daga abokan aikinsu.

Ko a baya ma shi ma mai bai wa shugaban kasar shawara na musamman kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu ya taba furta cewa a cikin jami'an tsaron akwai masu samar da makamai ga 'yanta'adda.

A kan hakan, Dakta Bulama, ya ce, hakan na nuna cewa lalle tsugune ba ta kare ba a wannan yaki : ''Domin wadanda ya kamata su yaki 'yanbindigan kenan sun juyo suna cin amana, suna yakar kasar.''

Ya ce: ''Tun a baya daman ana ta cewa akwai maciya amana amma za ka ga ba za a sa musu ido a bincika a kama su a hukunta su ba kowa ya gani.''

''Kuma idan aka ci gaba da wannan sai ka dauka to wannan maganar siyasa ce, ko kawai maganar banza ce ko kuma akwai sheda");