Abin da ya hana sulhu tsakanin Ecowas da Nijar - Tuggar

Amb. Yusuf Tuggar

Asalin hoton, Amb. Yusuf Tuggar/twitter

Watanni huɗu bayan kakaba wa jamhuriyar Nijar takunkumi da ƙungiyar Ecowas ta yi, sakamakon juyin mulkin sojoji, har yanzu ƴan ƙasar na ci gaba da ɗanɗana kuɗa da rayuwar ƙunci.

Farashin kayan masarufi ya yi tashin gwauron zabi, saboda rufe iyakar ƙasar da Najeriya ta yi, da kuma yanke hulɗar kasuwanci da ƙasashen Ecowas suka yi da Nijar.

A hirarsa da BBC, ministan harkokin wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, ya ce sun yi tayin tattaunawa domin kawo ƙarshen halin da ake ciki, amma hakan bai yiwu ba, don kuwa shugabannin sojoji da ke mulki a Nijar, sun ƙi amincewa da yunƙurin.

"Duk wata magana da ta shafi a saki Shugaba Bazoum, sun ce ba su amince ba. Sun ce kar ma a yi wannan maganar, kar ma a sa shi cikin sharuɗɗan yin sulhu," in ji Yusuf Tuggar.

Ya ce babu ta yadda za a iya samun sulhu a wannan yanayi.

"Za su ci gaba da rike shi kenan ya yi zaman dindindin a kulle");